Connect with us

Manyan Labarai

INA MATASAN SUKE?

Published

on

Wani matashi ne dan uwanku mai matsakaitan shekaru 20 zuwa 28 yayi tsokaci akan soyayya.

Ko da yake matsahin mai suna Bashir Sharfadi na ganin matukar aka gina soyayya akan wannan bincike nasa babu shakka za’a haigi d’a mai ido.

Ga nazatin nasa:

Abubuwa Biyar (5) da Zaka/kiyi Domin Mallake Zuciyar Budurwa/Saurayinki

Na danyi Nazari kadan inda na leka sashen su Nura Nakowa domin yau na kawo muku wasu hanyoyi da mutum zaibi a matsayinsa na wayayye domin ya sace zuciyar budurwarsa ba tare da farga ba, ko kuma shi ta sace tasa.

1. Abu na farko shine dolene masoya su mayar da junansu manyan abokai mafi kusanci, matukar baka zama babban aboki ga budurwarka ba ko ki zama babban aboki ga saurayinki to babu shakka akwai sauran aiki.
Ki dauki fadin Malam Umar M. Sharif da yake cewa “Zan Rayu dake zan mutu dake, Abadan dani dani dake zamu zauna” “Idan babu ke nima ba’a ganni ba, duk inda kike nan wurin amin marhaba…” ba wai ka daukeshi a wake ba a’a ka aikata shi a aikace, ka nuna kana matukar damuwa da ita, haka kema.

2. Ka zamo mai magana daya, kada ka/ki yiwa masa/ta karya duk abinda zaka fada ya zamo gaskiya, ya zama idan kika fada masa magana to baya shakku kada ki sake ki baiwa saurayinki damar kina fada masa magana yana yin shakku akanki, ko kana fada mata tana karyataka, matukar aka samu wannan kofar to hakika babu ranar dai-daituwa.

3. Girmama Juna, ya zama kina bashi girmansa, Namiji ko yaushe shi babbane kina ce masa Ranka ya dade, Yallabai da sunayen na Musamman na girmamawa, kaikuma namiji dolene ka dinga lallabata domin ita mace kullum ’yar shagwabace tana son ka dinga nuna mata kulawa sosai.

4. Ka Fahimceta ta Fahimceka, da yawa yanzu ana samun wannan matsalar mata basu tsayawa su fahimci dabi’un samarinsu ballantana su san ta yaya zasu mu’amalancesu, haka suma mazan basu fahimceta ba balle a samu dai-daito.

Yana da kyau ki fahimci abubuwan da yake so da wanda bayaso, shima kuma ya fahimci hakan akanki, hakan zai taimaka muku wajen kaucewa samun matsala, kuma indai kikayiwa namiji hakan to ba zai taba iya rabuwa dakeba, don wallahi ko yayi wata budurwar sai ya dawo.

5. Ki dinga bashi lokaci, ba wai ko yaushe baki da lokacinsa ba, haka shima, amman kada lokacin ya dinga wuce kima, ki dinga kiransa a waya (missed call) shima ya dinga kiranki, kar kuyi wasa da ZAFAFAN KALAMAI …

6. Ki dinga sanar dashi idan zakiyi wani abun wannan zaisa shima ya dinga kula dake akai-akai.

7. Kada ki dinga yawan rokonsa, kai kuma namiji tilasne ka dinga yi mata IHSANI wato kyautatawa tunda Hausawa sunce ai Kulawama Yabawace.

8. Ke dashi ku dinga yiwa juna Uzri, sannan ku dinga baiwa juna hakuri a duk sanda daya yayiwa day aba dai-dai ba.

A karshe manazarcin yayi fatan Soyayya mai dorewa, amma ko hangensa haka ne? Duba da cewa bai ko yi auren fari ba, kai hatta soyayyar ma ba yinta yake ba

Duk da cewa al’amari na rubutu baiwa ce, amma zamu so sanin ra’ayin matasa akan nazarin sa, da kuma saanin ko an karu da hujjoji da ya wassafo.

Manyan Labarai

Fadan dabar kofar Na’isa da kofar Dan-agundi, laifin iyaye – Mazaunin Yankin

Published

on

Wani mazaunin ƙofar Na’isa wanda ya buƙaci a sakaye sunansa, ya ce faɗan dabar da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa a yankin da Ɗan Agundi, laifin iyaye ne, da kuma wasu manya a unguwannin da ake zargin suna goya musu baya ta hanyar daƙile yunƙurin hukumomi na ɗaukar doka a kansu.

Mutumin ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, biyo bayan yadda rikicin faɗan dabar ya sake ɓarkewa a unguwannin a Alhamis ɗin nan, al’amarin da ya janyo asarar dukiyoyin al’umma a yankunan.

Ya ce lamarin ya faro ne tun a lokacin bikin ƙaramar Sallah, lamarin da a baya ƙura ta lafa, sai dai kuma a ranar Alhamis ɗin sai gashi an sake samun faɗan dabar.

A cewar sa, “A lokacin faɗan dabar ya faru an Sassari mutane da dama, hatta Saniya ma ba ta tsira ba sai da aka sareta, tare da fasa gilasan ababen hawan Mutane, “in ji shi”.

Sa dai mutumin ya ce, tuni jami’an tsaron Ƴan Sanda, suka kai ɗauki tare da kwantar da tarzoma, lamarin da ƙurar ta lafa.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ba za mu amince da yadda ake yawan kai wa jami’an mu hari ba a Kano – KAROTA

Published

on

Hukumar kula da zirgar-zirgar ababen Hawa ta jihar Kano, KAROTA, ta ce ba za ta lamunta da yadda ake yawan kai wa jami’anta farmaki ba, na ba gaira babu dalili yayin da suke gudanar da ayyukan su.

Shugaban Hukumar KAROTA, a Kano, Injiniya Faisal Mahmud Kabir, ne ya yi wannan gargaɗin ta cikin sanarwar da kakakin hukumar Abubakar Ibrahim Sharada ya aikowa tashar Dala FM Kano, a ranar Laraba 09 ga watan Afrilun 2025.

“Hakan na zuwa ne biyo bayan wani mummunan hari da wasu mutane da ke cikin baburin Adai-daita sahu suka kai wa jami’an na mu yayin da suke tsaka da aikinsu a titin da ke dab da gidan Buhari kan hanyar zuwa Gidan Zoo, “in ji shi“.

Sanarwar ta ce, tunda farko an tsayar da wani mai baburin Adai-daita Sahu ne inda yaƙi tsayawa, sai kawai aka hango mai ɗan sahun ya naushi jami’in karotar.

Sai dai a ta bakin Shugaban kungiyar ‘Yan Adai-daita Sahu a jihar Kano, ya ce waɗannan mutane ba halattattun ‘Yan Adai-daita Sahu ba ne, sun dai fake da sana’ar su dan aikata ta’addanci.

Daga bisani dai jami’n hulɗa da jama’a na Hukumar Koratar, Abubakar Ibrahim Sharada, ya ce hukumar za ta ɗauki tsattsauran mataki akan lamarin, don kare afkuwar irin hakan a gaba.

Hukumar ta ce duk wanda ya ga faruwar wani abu da ya shafe ta, ko kuma ƙorafe-ƙorafe, zai iya kiran waɗannan lambobin domin sanar da ita, da suka haɗar da 09015709449 ko 08059689422 ko kuma 08067311520.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ɗan Bijilante ya rasa ransa bisa arangamar su da wasu ƴan Daba a Kano

Published

on

Ƙungiyar sintirin Bijilante ta ƙasa reshen jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin kwamandan ta Ubale Barau Muhammad Badawa, ta tabbatar da rasuwar guda daga cikin jami’in ta mai suna Suraj Rabi’u mazaunin Jaba da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar, sakamakon arangama da ƴan Daba.

Mai magana da yawun ƙungiyar Bijilante na jihar Kano, kuma Kwamandan ta na ƙaramar hukumar Fagge, Usman Muhammad Ɗan Daji, shi ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM Kano a ranar Lahadi.a

“Jami’in Bijilanten namu ya rasa ran nasa ne sakamakon arangama da suka yi da wasu Ƴan Daba yayin gudanar aikinsu a ranar Idin ƙaramar Sallah, inda ƴan dabar suka soke shi da Ɗanbida a Ƙirji da bayansa, wanda ya yi sanadiyar rasuwarsa, “in ji Usman”.

Ya kuma ce, an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi mai suna Usman Sharif mazaunin ƙaramar hukumar Dala, kuma tuni aka miƙa shi hannun jami’an tsaro.

Usman Ɗan daji, ya kuma yi addu’ar Allah ya jiƙan jami’in nasu ya gafarta masa.

Continue Reading

Trending