Manyan Labarai
Yadda Manhajar Whatsapp ta hada kan Sha’arai- Yan Biyun Ma’aiki

Hassana da Usaina da akafi sani da ‘yan biyun ma’aiki’ sunyi shura a fannin yabon ma’aiki a kano, inda wakokin su suka shiga sahun wakoki na yabo da matasa ke sauraro a kasashe da harshen hausa ya yadu.Cikin shirin Gari na masoya Manzon Allah da Sayyadi Bashir Dandago ke gabatar wa a wannan tasha, matasan sun ce babu wani abu daya kawo su waje guda kamar manhajar whatsapp.Mawakan sunyi magana akan taron karawa juna sani da suke shiryawa duk shekara mai taken Da’irar Sha’iran Annabi, wanda suka shirya gudanarwa ranar lahadi 8 watan Muharram shekara ta 1441a.h, wannan dai itace shekara ta biyu da fara wannan taro da ya tattaro kan sha’irai daga sassa duniya inki ciki har da jamhuriyar Nijar.KOWANNE CIGABA SUKA SAMU A YABON ANNABI?Sun samu nasarori da suka hadar da hadin kan sha’irai, da ya haifar da karin fahimtar juna tsakanin sha’irai maza da mata.Sai wakar da suka yi yadda ta hado sha’irai sama da 100 a bangarorin biyu, mai tasiri ga kafafen yada labarai da aka yiwa lakabi da “Ga sha’iran annabi.”Wannan sune kadan daga cikin nasarori da muka samu inji yan biyun ma’aiki.Sayyadi Bashir Dandago dai ya kasance yana zakulo fitattun Sha’irai afagen yabon ma’aiki dukkanin ranakun juma’a, domin ganawa da masu sauraro har su amsa tambayoyi kan wakokin su.
Babban burin shirin na Kano Gari Na Msoya Mazon Allah a cewar mai gabatrwaar bai wuce fito da hikimomi dake kunshe cikin masana’antar yabo ba.

Manyan Labarai
Zargin Baɗala: Hisbah ta kama masu zance cikin Mota a Kano

Hukumar Hisbah ta jihar Kano, ta kai sumame wani gidan biki, inda ta samu nasarar kama wasu masu zance a cikin Mota, suna aikata abinda bai kamata ba.
Mataimakin babban kwamandan hukumar a jihar Kano, Dakta Mujahideen Aminudden Abubakar, shi ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da wakilin Dala FM Kano, Adam Abubakar Indallahi, a ranar Lahadi.
“Mun samu nasarar ne ƙarƙashin jagorancin jami’ansu na ofirashin gyara kayan ka, yayin zagayen da suka gudanar a unguwar Kurna da filin Durumi da gwammaja, inda suka tashi masu bikin tare da kama wasu Samari da Ƴan mata da zargin suna aikata abinda bai dace ba a cikin Mota, “in ji shi”.
Ya kuma ƙara da cewa, sun jami’an nasu sun kuma kama wasu da ake zargin suna aikata Baɗala akan babur mai kafa biyu samfurin roba-roba.

Manyan Labarai
Siyasantar da Tsaro ne ke ƙara ta’azzara faɗan Daba a Kano – Masanin Tsaro

Yayin da faɗan Daba ke ƙara zama alaƙaƙai tsakanin al’umma a sassan birnin Kano, masanin tsaron nan Ditective Auwal Bala Durumin Iya, ya ce matuƙar ana son a daƙile lamarin, sai gwamnati ta cire Siyasantar da tsaron, tare da bai wa jami’an tsaro haɗin kan da ya dace.
Ditective Auwal Bala ya bayyana hakan ne a zantawar sa da tashar Dala FM, a lokacin da yake tsokaci kan hanyoyin da za a bi domin daƙile rikice-rikicen faɗan dabar da ƙwacen Waya da kuma daƙile Shaye-shayen kayan maye a jihar.
“Baya ga batun bai wa jami’an tsaro haɗin kan, da kuma wadata su da kayan aiki, akwai kuma buƙatar suma al’umma su rinƙa bai wa jami’an tsaron bayanan sirri, don kawo karshen faɗan dabar a faɗin jihar Kano, “in ji shi”.
Ditective Durumin Iya, ya ƙara da cewar, suma Ƴan Siyasa ya kamata su kaucewa siyasantar da harkokin Tsaro, da gujewa ɗaukar nauyin Ƴan Dabar, ko kuma fito dasu idan aka kamasu, saboda hakan yana taka rawa wajen ƙara ta’azzara Ayyukan Daba.
Jihar Kano dai, ta yi ƙaurin suna wajen fuskantar rikice-rikicen faɗan Daba, da ƙwacen Waya, da kuma sha da dillancin kayan maye, ko da dai tuni hukumomi suka tashi haiƙan domin magance matsalolin.

Manyan Labarai
Jarabawar JAMB: An dakatar da duban tsaftar muhalli na watan Afrilun 2025 – Gwamnatin Kano

Gwamnatin jihar Kano ta dakatar da aikin duban tsaftar muhalli na watan Afrilun 2025, domin bai wa ɗaliban da za su rubuta jarrabawar shiga manyan makarantun kasar nan JAMB, damar isa cibiyoyin zana jarrabawar a kan lokaci.
Kwamishinan muhalli da kula da sauyin yanayi na jihar Kano Dakta Dahir Hashim Muhammad ne ya sanar da hakan, a cikin wata sanarwa da daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar Sama’ila Garba Gwammaja ya fitar a ranar Alhamis.
Sanarwar ta ce, an dauki wannan matakin ne bayan nazari da tuntubar masu ruwa da tsaki, a kokarin bai wa daliban jihar Kano damar rubuta jarabawarsu ta JAMB, ba tare da wata matsala ba.
“Muna mai tabbatar wa mazauna Kano cewa, dakatarwar duban tsaftar muhallin na wucin gadi ne a iya wannan watan kawai, kuma za a ci gaba da aikin tsaftar muhallin a watan Mayun 2025, “in ji Dr. Ɗahir”
Kwamishinan ya kuma yi kira ga mazauna jihar Kano, da su ba hukuma hadin kai da fahimtar dalilin da ya sa aka yanke wannan hukunci, musamman na ganin cewa ayyukan tsaftar muhalli ba su ci karo da wasu muhimman abubuwan da ke faruwa a jihar ba.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su