Connect with us

Manyan Labarai

Yadda magagin mutuwa ya sa Jaki burma katanga

Published

on

Labarin jakin nan da wani matashi ya sokawa wuka kusan mun kawo muku shi a makon daya gabata.

Koda yake mummunan yanayi da jakin ke ciki shine babban abinda ya fi tayar da hankali.

Bayan shafe daren juma’a cikin rai kokwai mutu kwakwai, rai yayi halin sa a ranar Asabar da sassafe.

Rahotanni daga unguwar Jaen dake yankin karamar hukumar Gwale a Kano, sun bayyana cewar sai da ta kai jakin ya burma katangar gidan su cikin magagin fitar rai

Wanda ake zargi da aikata laifin ya gurfana gaban kotun majistare dake kan titin gyadi gyadi domin amsa tuhume tuhumen da ake masa

Ana zargin Bashir dan shekaru 23 da laifin kutse cikin gida da kuma haddasa rauni, tuhumar nan take ya amsa ba tare da wahalshe da sharia ba.

Daga nan mai shari’a Auwal Yusuf Usman ya bayar da umarni ga yan sanda su koma da matashin wajensu domin fadada bincike zuwa ranar Talata.

A ranar jum’ar data gabata ne Bashir ya kutsa gidan makocinsu mai suna Mallam, ya farwa kanwar sa mai suna Fatima yar kimanin shekaru 18 da suka da wuka, inda ta samu raunuka a kafada da fuska, da kuma gefen ciki.

Shaidun gani da ido sun ce Bashir ya so yiwa Fatima yankan rago ne inda ya take ta a kasa, amma ta samu taimako daga wata babbar yayar ta inda ta rike wukar, da a karshe itama aka zuge mata hannu.

Ance Bashir ya samu tallafin abokin sa wanda yanzu haka ake nema ruwa a jallo, bayan sun fito daga gidan su Mallam sai suka farwa jakin sa dake kofar gida da sara, inda hanjin sa ya burtso waje.

Wanda safiyar Asabar data gabata jakin ya mutu, bayan shafe tsawon dare cikin numfarfashi sama sama.

Manyan Labarai

Ƙarin albashin da gwamnatin tarayya ta yiwa ma’aikatan ta ci gaban mai haƙan rijiya ne – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Universal Declaration of Human Rights, ta ce ƙarin albashin da gwamnatin tarayya ta yiwa ma’aikatan ta, ci gaban mai haƙan rijiya ne, domin ba zai magancewa ma’aikatan matsalolin su ba.

Daraktan ƙungiyar reshen jihar Kano Alhaji Umar Sani Galadanci, ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da wakilinmu na ƴan Zazu Hassan Mamuda Ya’u, a yau Laraba, lokacin da yake tsokaci a kan bikin ranar ma’aikata da ake gudanarwa yau a Najeriya.

Ya kuma ce kasancewar ƙarin albashin ba zai ragewa ma’aikatan wata damuwa ba, sai dai ma ya tunzura ma’aikatan, bai kamata ƙungyoyin ƙwadago su amine da tsirarun ƙarin ba.

“Matukar gwamnatin tarayya za ta rinƙa tunzura ma’aikata da irin wannan tsirarun albashin babu makawa zamu gurfanar da ita a gaban kotu, “in ji Galadanci”.

Umar Sani ya kuma shawarci gwamnatin tarayya da ta lalubo sabbin hanyoyi da za’a ƙarawa ma’aikatan albashi mai tsoka wanda zai rinƙa magance musu wasu matsalolin su na yau da kullum.

Har ila yau, suma ƙungiyoyin ƙwadago a ƙasar nan, sun yi fatali da ƙarin albashin da gwamnatin tarayya ta yiwa ma’aikatan ta da kashi 25 cikin ɗari, da kuma kashi 35 a cikin ɗari.

Ƙungiyoyin ƙwadago da dama na NLC, da TUC, da sauran ƙungiyoyi ne suka gudanar da taron ranar ma’aikan a sassan jahohin ƙasar nan.

Continue Reading

Manyan Labarai

Kayan aikin ginin da ya ruftawa magina a Kuntau ba masu inganci ba ne – Cibiyar masu Taswirar Zane-zanen Muhalli

Published

on

Cibiyar masu tasawirar zane-zanen muhalli ta ƙasa reshen jihar kano, tayi Allah wa dai da kayan da akayi wani ginin Bene da shi mai hawa uku, da ya faɗo akan wasu magina a cikin unguwar Kuntau da ke yankin karamar hukumar Gwale a jihar kano.

Mataimakin shugaban ƙungiyar na kasa Arct Ali Mukhtar, ne ya bayyana hakan a lokacin da cibiyar takai ziyara wajen da al’amarin ya faru.

Ya ce dukkanin kayan da aka yi aikin ginin benen da su ba masu inganci ba ne.

A nasa jawabin shugaban cibiyar a nan nano Arct Bashir Hassan Hanga, kira ya yi ga gwamnatin jihar kano, da ta hana duk masu irin wannan gine-gine ba tare da sahalewar hukumar tsara birane ba wato Knupda, ta kuma ɗauki mataki akan mamallakin wannan gini da ya rushe a kan maginan.

Wakilin mu Shamsu Dau Abdullahi ya rawaito cewa dukkanin tawagar cibiyar tsara gine-ginen, sun ce za su ziyarci asibitin Murtala Muhammad, domin duba mutanen da gini ya fadowa da kuma zuwa ta’aziya gidan waɗanda suka rasu su uku.

Continue Reading

Manyan Labarai

Majalisa ta amince da dokar gwajin cutar Ƙanjamau da ta Sikila kafin aure a Kano

Published

on

Majalisar Dokokin jahar kano ta amince da dokar yin gwajin cutar kanjamau da ta Sikila da kuma sauran cututtuka kafin yin aure.

Da yake Jawabi akan kafa dokar, Shugaban Majalisar dokokin jahar kano Alhaji Jibril Isma’il Falgore, ya ce dokar za ta daƙile yaɗuwar cututtuka a tsakanin ma’aurata da yaɗa su ga iyali da ma al’umma baki ɗaya.

Har ila yau, dokar ta ba da damar yin gwajin cututtuka masu haɗari da wuyar magani kafin yin aure, tare da tanadin hukunci mai tsanani ga duk wanda yaƙi yin biyayya ga dokar.

Mataimakin Akawun Majalisar kuma babban Sakatare Alhaji Nasiru Magaji, ne ya gabatar da karatu na uku akan dokar kafin amincewa da ita a ranar Litinin.

Continue Reading

Trending