Connect with us

Nishadi

Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna

Published

on

Mansura Isah tayi kaca-kaca da Sadiya Haruna

Fitacciyar jaruma kuma mai shirya fina-finai a masana’antar Kannywood Mansura Isah ta nuna takaicin ta kan abinda ya faru tsakanin Sadiya Haruna da kuma jarumi Isah A. Isah.

A kwanakin baya dai an hangi Mansura Isah tare da Sadiyar a cenima cikin raha da annashuwa.

Sai dai a wannan rigimar da ta faru tsakanin Isah da sadiya, Mansurar ta nuna rashin jin dadinta.

Har ma ta wallafa wani rubutu da turanci a shafinta na instagram cewa “Sadiya Haruna ba zan iya sanya hotonki koda a shafina ba, domin naji kunyar abin da kika aikata.

Sannan ta kara da cewa “ Subhanallahi! Sadiya ba na tausayin ki ko kadan wallahi ban damu dake ba, domin kin yankewa kanki rayuwar da kike so da halin da kike so ki tsinci kanki, damuwa ta daya ce yaranki a wadanda za ki haifa nan gaba.

Duk abinda mukayi yana nan a social media har abada ko da kuwa kin goge abinda kika wallafa

Ba zance ba zaki samu mijin aure ba domin akwai masu Imani, amma kiyi tunanin zagin da za’a yiwa yaranki idan sunyi fada ada mutane za’a tuna musu abinda mamansu tayi lokacin tana budurwa.

Na san Allah ne mai shiyarwa kuma za ki iya shiryuwa amma kiyi tunani kalubalen da iyalinki da ‘ya’yanki za su fuskanta.

Mansura Isah dai ta yi dogon bayani game da wannan rikici daya faru tsakanin jaruman biyu.

Tuni dai ‘yansanda suka bada belin Sadiya Haruna kuna suna cigaba da bincike.

Nishadi

Rayuwa ta ba ta da wata ma’ana a yanzu — Wizkid

Published

on

Guda daga cikin fitattun mawakan nan na Afrobeats, Ayodeji Balogun, wanda aka fi sani da Wizkid, ya bayyana cewa rayuwa ba ta da wata ma’ana a gare shi tun bayan mutuwar mahaifiyarsa, Misis Jane Dolapo Balogun.

Mawaki Wizkid ya bayyana halin da ya ke ciki a kafafen sada zumunta tun bayan mutuwar ta ta, inda ya ce rayuwarsa sam babu dadi bayan mutuwar mahaifiyar tasa.

Ta cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Instagram a ranar Laraba, mawakin ya bukaci masoyansa da su bi Ubangiji.

Jaridae Daily Trust ta ruwaito yadda mawakin ya rasa mahaifiyarsa a watan Agustan 2023, a lokacin da yake kan bulaguron wakokin sabon kundin wakarsa mai suna ‘More Love Less Ego’ a Turai.

Ya rubuta, “Kwanaki bayan na rasa mahaifiyata; Rayuwa ba ta da ma’ana! Amma mun ji. Wani lokaci dole ne ku bar komai ya tafi. A bi Ubangiji kawai, “A cewarsa”.

Rahotanni sun bayyana cewa a ranar Talata, Wizkid ya tayar da hankula a tsakanin magoya bayansa, bayan da ya wallafa hoton sa yana gadon asibiti a shafinsa na Instagram a cikin wani yanayi.

A cikin hoton dai mawakin ya yi nuni da cewar za’a duba shi, amma bai bayyana mai yake samunsa ba, lamarin da ya haifar da cece-kuce a shafun na sada zumunta.

Continue Reading

Nishadi

Na yi asarar dala biliyan 2 a rana ɗaya kuma har yanzu ina raye – Mawakin Amurka

Published

on

Ba’amurke kuma mawaki, Kanye Omari West, wanda aka fi sani da Kanye West ko Ye, ya yi asarar dala biliyan 2 a cikin sa’o’i 24, bayan wasu kamfanoni da dama sun yanke alaka da shi saboda kalaman kyamar Yahudawa.

Wannan na zuwa ne kasa da sa’o’i 48, bayan wata mujallar kasuwanci ta Amurka, Forbes, ta sanar da cewa Kanye ba shi da wani matsayi a cikin jerin masu kudi a yanzu bayan da yarjejeniyarsa mai tsoka da Adidas ta yanke hulda da shi.

Kamfanonin da suka yanke alaƙa da Kanye ya zuwa yanzu sun haɗa da Balenciaga, MRC (dakin nishaɗin da aka riga aka gama Ye Documentary), hukumar baiwar sa CAA, Adidas, Jaylen Brown da Aaron Donald, Foot Locker, The RealReal, T.J. Maxx, Madame Tussauds.

Da yake mayar da martani kan asarar, mawakin, a wani sako da ya wallafa a shafin Instagram, ya bayyana cewa mutanen shi ne, ba kudin ba.

Ya rubuta, “Na yi asarar dala biliyan 2 a rana ɗaya, kuma har yanzu ina raye. Wannan maganar soyayya ce, har yanzu ina son ku; kudin ba ni ba ne, jama’a su ne ni.”

Har ila yau, makarantarsa, Donda Academy, abun ya shafa ta, yayin da aka fitar da su daga gasar makarantar sakandare saboda maganganun Kanye.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

Magen gidan Firaministar Birtaniya na dakon uwar dakin ta

Published

on

A yau ne iyalan tsohon firaministan Burtaniya Boris Johnson ke tattara komatsansu a shirye-shiryen da suke yi na bankwana da gidan firaministan wanda ke Downing Street, domin bayar da waje ga sabuwar firaministar Mrs Liz Truss tare da iyalanta, wacce za ta ci gaba da zama a gidan na tsawon mulkinta,

To sai dai yayin da ake wannan shiri na ficewa daga gidan Kyanwar gidan mai suna ‘Lary’ na nan daram a gidan tana jiran isowar sabuwar firaministar

A rahoton BBC sun ce, Lary wacce ba mallakin kowa ba ce, ta zama babbar Kyanwar gidan firaminstan Birtaniya.

Kyanwar mai shekara 15, wacce ta yi zamani da firaministocin Burtaniya har guda uku, na shirin zama da iyalan Mrs Truss.

Continue Reading

Trending