Connect with us

Nishadi

Abinda ya sanya jaruma Barauniya rushewa da kuka

Published

on

A wani bangaren kuwa juruma Hafsat Idris wadda aka fi sani da Barauniya ta fashe da kuka a yayin da tsohon sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya sanata Shehu Sani ke bata kyautar Face of Kannywood da ta lashe a gasar City Movie Award ta bana da aka gabatar a birnin Lagos.

Tun da farko dai Jarumar ta rufe fuskarta yayin da yake bata kyautar, inda bayan da ta karba aka mika mata abin Magana kawai sai ta rushe da kuka tana mai godiya bisa karramawar da aka yi mata.

Wannan batu dai ya dauki hankulan masoyanta da dama, inda suka rika bayyana mabambamtan ra’ayoyi kan hakan a shafukan sada zumunta.

RUBUTU MASU ALAKA:\

Yiwa matarka kallon kurilla yana kara yawan shekaru.

Gwamnati bata bincikar masu uwa a gindin murhu -Kwamaret Bello Basi

Munyi hannun riga da rashawa- Hisba

Labarai

Kannywood:- MOPAN za ta fara raba ID CARD

Published

on

Hadaddiyar kungiyar masu shirya fina-finai ta Mopan na sanar da dukkanin wadanda sukayi rijista cewa za ta fara bayar da shaida wato ID CARD ga masu bayar da umarni, da masu shirya fina-finai da masu daukar hoto me motsi cewa za’a fara basu ID CARD daga ranar 25 ga wannan wata.

 

Cikin sanarwa da shugaban kungiyar na kano Ado Ahmad Gidan Dabino ya fitar, ya ce bayar da ID CARD din ya shafi iya wadanda aka ambata ne kadai banda jarumai.

 

A cewar sa shaidar su ma Jarumai za’a fara bayar da nasu da zarar an kammala tantance su.

 

A don haka ƙungiyar ta MOPPAN ke sanar da dukkanin wadanda aka ambata da su ka tabbatar sunyi rijista da su je ofishin kungiyar domin karbar ID CARD.

Continue Reading

Nishadi

Rayuwa ta ba ta da wata ma’ana a yanzu — Wizkid

Published

on

Guda daga cikin fitattun mawakan nan na Afrobeats, Ayodeji Balogun, wanda aka fi sani da Wizkid, ya bayyana cewa rayuwa ba ta da wata ma’ana a gare shi tun bayan mutuwar mahaifiyarsa, Misis Jane Dolapo Balogun.

Mawaki Wizkid ya bayyana halin da ya ke ciki a kafafen sada zumunta tun bayan mutuwar ta ta, inda ya ce rayuwarsa sam babu dadi bayan mutuwar mahaifiyar tasa.

Ta cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Instagram a ranar Laraba, mawakin ya bukaci masoyansa da su bi Ubangiji.

Jaridae Daily Trust ta ruwaito yadda mawakin ya rasa mahaifiyarsa a watan Agustan 2023, a lokacin da yake kan bulaguron wakokin sabon kundin wakarsa mai suna ‘More Love Less Ego’ a Turai.

Ya rubuta, “Kwanaki bayan na rasa mahaifiyata; Rayuwa ba ta da ma’ana! Amma mun ji. Wani lokaci dole ne ku bar komai ya tafi. A bi Ubangiji kawai, “A cewarsa”.

Rahotanni sun bayyana cewa a ranar Talata, Wizkid ya tayar da hankula a tsakanin magoya bayansa, bayan da ya wallafa hoton sa yana gadon asibiti a shafinsa na Instagram a cikin wani yanayi.

A cikin hoton dai mawakin ya yi nuni da cewar za’a duba shi, amma bai bayyana mai yake samunsa ba, lamarin da ya haifar da cece-kuce a shafun na sada zumunta.

Continue Reading

Nishadi

Na yi asarar dala biliyan 2 a rana ɗaya kuma har yanzu ina raye – Mawakin Amurka

Published

on

Ba’amurke kuma mawaki, Kanye Omari West, wanda aka fi sani da Kanye West ko Ye, ya yi asarar dala biliyan 2 a cikin sa’o’i 24, bayan wasu kamfanoni da dama sun yanke alaka da shi saboda kalaman kyamar Yahudawa.

Wannan na zuwa ne kasa da sa’o’i 48, bayan wata mujallar kasuwanci ta Amurka, Forbes, ta sanar da cewa Kanye ba shi da wani matsayi a cikin jerin masu kudi a yanzu bayan da yarjejeniyarsa mai tsoka da Adidas ta yanke hulda da shi.

Kamfanonin da suka yanke alaƙa da Kanye ya zuwa yanzu sun haɗa da Balenciaga, MRC (dakin nishaɗin da aka riga aka gama Ye Documentary), hukumar baiwar sa CAA, Adidas, Jaylen Brown da Aaron Donald, Foot Locker, The RealReal, T.J. Maxx, Madame Tussauds.

Da yake mayar da martani kan asarar, mawakin, a wani sako da ya wallafa a shafin Instagram, ya bayyana cewa mutanen shi ne, ba kudin ba.

Ya rubuta, “Na yi asarar dala biliyan 2 a rana ɗaya, kuma har yanzu ina raye. Wannan maganar soyayya ce, har yanzu ina son ku; kudin ba ni ba ne, jama’a su ne ni.”

Har ila yau, makarantarsa, Donda Academy, abun ya shafa ta, yayin da aka fitar da su daga gasar makarantar sakandare saboda maganganun Kanye.

Continue Reading

Trending