Connect with us

Manyan Labarai

Muna zargin aikata masha’a a Kannywood. -Hisba

Published

on

Hukumar Hisba tace ta samu rahoton yadda ake cin karo da tarin kwaroron roba a wasu masana’antu na shirya fina finai ta kannywood dake kan titin gidan Zoo anan kano.

Rahoton a cewar hisbar ya gano yadda masu shara ke cin karo da robar a lunguna da taurarin masana’antar ke taruwa domin gudanar da harkokin su musamman da maraice, sai dai kuma ba’a kama sunayen wuraren ba a fili ba.

Koda yake Hisba tayi zargin wasu daga cikin yan fim din ne ke aikata masha’a da irin matan da kan baro garuruwan su domin sha’awar zamowa taurarin fina finan hausa.

Hisbbar tace tayi arba da wata matashiya data fado hannun hukumar, har take shaidawa jami’anta cewar tazo Kano ne wajen jaruma Maryam Yahaya, bayan haduwar su a facebook.

Zuwan nata kuma yana da alaka da irin sha’awar da matashiyar ta nunawa jarumar na zamowa tauraruwa.

Babban mataimaki a hukumar Muhammad Al-bukari Mika’ilu ya ce abun da wasu ‘Yan film din ake zargin suna yiwa matan da suke son shiga film din Kannywood yafi kama da karuwanci ba kasuwanci ba.

Al-bukari yace zasu gayyaci shugabannin kungiyar domin tattaunawa kan wadannan zarge zarge, da kuma tabbatar da daukar matakai da zasu kai ga dakile duk wani yunkurin aikata fasadi a masana’antar.

Dangane da batun da matashiyar tayi kan haduwar su da Maryam Yahaya a facebook, mun tuntubi Maryam Yahaya ta wayar tarho domin jin hanzarin ta, wanda kawo yanzu ba tace uffan ba.

Sai dai a nasa bangaren shugaban kungiyar Kannywood Kabiru mai kaba yace a shirye suke su baiwa hukumar hisba hadin kai da take nema, domin hukunta masu aikata badalar matukar ta tabbata cewa ana yi din kuma ‘Yan kungiyar ne.

Wakilin mu Ibrahim Abdullahi Soron-dinki ya rawaito cewa tuni aka tisa keyar budurwar da tazo gurin Maryam Yahaya zuwa Kaduna, domin danka ta a hannun mahaifanta.

Manyan Labarai

Da na hadu da kwankwaso da sai na mare shi – Ganduje

Published

on

Tsohon Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje yace da sun hadu da kwankwaso da akwai yiyuwar ya mare shi, a fadar shugaban kasa.

Tsohon Gwamnan ya bayyana Hakan ne yayin wata ganawa da gidan television na channels, yayin da yake martani Kan ganawar shugaban kasa Asuwaju Bola Ahmad Tinubu da Kuma jagoran jam’iyyar NNPP Sanata Rabiu Musa Kwankwaso a yammacin wannan juma’a.

” Nasan yana gidan Amma bamu hadu ba, da mun hadu akwai yiyuwar na kwada masa Mari” inji Ganduje.

Idan za’a iya tunawa dai kwanakin baya shugaban kasa Asuwaju Bola Ahmad Tinubu yayi wata ganawa da kwankwaso, lamarin da aka jiyo tsohon Gwamnan na korafi cewa ba’a Yi musu adalchi ba, Koda dai a wancan lokaci, Ganduje ya musanta, ta bakin tsohon kwamishinan yada labarai Muhammad Garba, inda yace ba muryar Ganduje bace.

Wannan dai na zuwa ne a Gabar da gwamnatin Kano ke cigaba da rushe wuraren da tayi zargin gwamnatin baya ta Abdullahi Umar Ganduje ta cefanar ba bisa ka’ida ba.

Continue Reading

Manyan Labarai

Gargadin Gwamnatin Kano Kan masu kaya a wuraren gwamnati

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta gargadi dukkanin masu kaya a wuraren da tayi zargin gwamnatin baya ta cefanar ba bisa ka’ida ba, dasu kwashe kayan su cikin gaggawa.

Cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin Dakta Abdullahi Baffa Bichi ta fitar ta bayyana cewa, dukkanin masu kaya a shagunan da aka gina a jiki ko cikin makarantu, Maƙabartu, Asibitoci, Masallatai, gefen badala, Filayen ma’aikatu, Filayen wasanni da sauran wuraren shakatawa mallakin gwamnati da cewa suyi gaggawar kwashe dukkanin kayan su dake cikin shagunan da aka gina a waƴannan gurare ba tare da ɓata lokaci ba.

Continue Reading

Manyan Labarai

Abba Gida Gida ya fara rusau

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta fara rushe wasu gine gine da aka yi su a wuraren gwamnati Ba bisa ka’ida ba.

A cikin daren Asabar din nan ne tawagar Kwamitin kar ta kwana mai lura da rushe gine gine ta fara da rushe wani sabon rukunin shaguna mai kunshe da sama da shaguna 90 dake jikin filin sukuwa a jihar Kano.

Mai magana da yawun gwamnan Kano Sunusi Ahmad Bature Dawakin Tofa ya bayyana cewar wannan aiki somin tabi ne domin batun rushe gine ginen da aka yi su akan filayen jama ar Kano lamari ne da babu gudu babu ja da baya kamar yadda gwamna Engr Abba Kabir Yusif ya bayyana a lokacin da yake yakin neman zabe.

Tawagar kwamitin na kar ta kwana zai cigaba da rushe dukkan wasu gine gine da aka yi su ba bisa kaida ba.

Continue Reading

Trending