Connect with us

Manyan Labarai

Muna zargin aikata masha’a a Kannywood. -Hisba

Published

on

Hukumar Hisba tace ta samu rahoton yadda ake cin karo da tarin kwaroron roba a wasu masana’antu na shirya fina finai ta kannywood dake kan titin gidan Zoo anan kano.

Rahoton a cewar hisbar ya gano yadda masu shara ke cin karo da robar a lunguna da taurarin masana’antar ke taruwa domin gudanar da harkokin su musamman da maraice, sai dai kuma ba’a kama sunayen wuraren ba a fili ba.

Koda yake Hisba tayi zargin wasu daga cikin yan fim din ne ke aikata masha’a da irin matan da kan baro garuruwan su domin sha’awar zamowa taurarin fina finan hausa.

Hisbbar tace tayi arba da wata matashiya data fado hannun hukumar, har take shaidawa jami’anta cewar tazo Kano ne wajen jaruma Maryam Yahaya, bayan haduwar su a facebook.

Zuwan nata kuma yana da alaka da irin sha’awar da matashiyar ta nunawa jarumar na zamowa tauraruwa.

Babban mataimaki a hukumar Muhammad Al-bukari Mika’ilu ya ce abun da wasu ‘Yan film din ake zargin suna yiwa matan da suke son shiga film din Kannywood yafi kama da karuwanci ba kasuwanci ba.

Al-bukari yace zasu gayyaci shugabannin kungiyar domin tattaunawa kan wadannan zarge zarge, da kuma tabbatar da daukar matakai da zasu kai ga dakile duk wani yunkurin aikata fasadi a masana’antar.

Dangane da batun da matashiyar tayi kan haduwar su da Maryam Yahaya a facebook, mun tuntubi Maryam Yahaya ta wayar tarho domin jin hanzarin ta, wanda kawo yanzu ba tace uffan ba.

Sai dai a nasa bangaren shugaban kungiyar Kannywood Kabiru mai kaba yace a shirye suke su baiwa hukumar hisba hadin kai da take nema, domin hukunta masu aikata badalar matukar ta tabbata cewa ana yi din kuma ‘Yan kungiyar ne.

Wakilin mu Ibrahim Abdullahi Soron-dinki ya rawaito cewa tuni aka tisa keyar budurwar da tazo gurin Maryam Yahaya zuwa Kaduna, domin danka ta a hannun mahaifanta.

Manyan Labarai

Babu ɗaga Ƙafa tsakanin mu da Ƴan Daba da masu ƙwacen Waya a Kano – Anty Snaching Phone

Published

on

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Wayoyin jama’a da kuma daƙile Shaye-shayen kayan maye ta Anty Snaching Phone, ta gargaɗi matasan da suke addabar al’umma da faɗan Daba a cikin birnin jihar Kano, da su ƙauracewa hakan domin ba za su saurarawa dukkanin wanda ya faɗa komar su ba.

Kwamandan rundunar tsaron a jihar Kano Inuwa Salisu Sharaɗa, shi ne ya bayyana hakan a zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, ya ce duk wanda suka kama da laifi musamman ma na faɗan Daba, ko ƙwacen waya ko kuma sha da dillancin kayan maye, za a ɗauki tsattsauran mataki akan sa.

 

“Babu ɗaga ƙafa tsakanin mu da masu ƙwacen Wayoyin jama’a, da Faɗan Daba, da kuma masu Sha da dallancin kayan Maye a jihar Kano, kuma duk wanda mu ka kama sai mun miƙa shi gurin da ya dace don ɗaukar Mataki, “in ji Inuwa Sharaɗa”.

 

Ya kuma buƙaci iyaye da su ƙara sanya idanu wajen kula akan shige da ficen ƴaƴan su, ta yadda za su zama ababen koyi a tsakanin al’umma.

Continue Reading

Manyan Labarai

Za’a hukunta duk ma’aikacin Shari’ar da aka samu da laifi – Babbar Jojin Kano

Published

on

Babbar jojin Kano mai Shari’a Dije Abdu Aboki, ta jaddada cewar kwamitin ladabtarwa na hukumar Shari’a a jihar, zai hukunta duk wani ma’aikaci a tsagin Shari’a matuƙar aka same shi da laifin cin-hanci da rashawa.

Mai Shari’a Dije Aboki ta bayyana hakan ne a yayin taron ƙarawa juna sani wanda hukumar shari’ar ta gudanar ranar Talata, a ɗakin taro na Murtala Muhammad Library da ke Kano.

Taron an shirya shi ne don tunasar da sabbin ma’aikatan Shari’a, akan nauyin da ya hau kan su don mayar da hankali sosai akan batun gujewa cin-hanci da rashawa.

Babbar mai Shari’ar Dije Abdu Aboki, ta bayyana cewar akwai takaddu masu ɗauke da lambobin wayarta da aka liƙe a bangon kotuna, kuma duk wanda aka yi wa ba dai-dai ba zai iya sanar da ita ta kan lambobin kuma za a dauki mataki akan duk ma’aikacin da aka samu da laifi.

Wakilin tashar Dala FM Kano, Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, a yayin taron taron ma’aikatan Shari’a da al’umma da dama ne suka samu damar halarta.

Continue Reading

Hangen Dala

Rashin wuta: Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Published

on

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.

Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.

Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.

Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.

Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.

Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.

Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.

Continue Reading

Trending