Connect with us

Nishadi

An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su

Published

on

Mahukunta a makarantar Farfesa Ango Abdullahi dake Zaria, sun tabbatar da cewa jarumin fina-finan Hausa Adam A. Zango ya dauki nauyin karatun dalibai marayu guda 101 a makarantar.

Yayin tattaunawar da Dala FM tayi da shugaban makarantar Mallam Hamza Jibril ya tabbatar mana da cewa sun samu takarda daga dauke da bayanan cewa Adam Zango yana son zai dauki nauyin karatun dalibai har guda 101, kuma bayan da suka gama tattaunawa tuni Adam Zangon ya biya kudin tun a makon da ya gabata.

Hotunan takardun shaidar biyan kudin da Adam Zango yayi.

Dangane da daliban da za’a dauki nauyin karatun nas Mallam Hamza ya bayyana cewa Adam Zango ya baiwa masarautar Zazzau gurbin mutane 50 sai jam’iyyar APC aka bata gurbin mutane 31 sai kuma jam’iyyar PDP da aka baiwa mutane 20.

Dukkan su bisa sharadin zasu kawo dalibai marayu, ko talakawa da iyayen su basu da ikon biya musu kudin makaranta.

Haka zalika Mallam Hamza ya karyata dukkan rahotonnin dake yawo a soshiyal midiya na cewa batun daukar nauyin karya ne ba gaskiya bane.

Duk kokarin da Dala FM tayi na jin ta bakin jarumin Adam A. Zango amma abin ya ci tura, sai dai wani makusancinsa ya tabbatar mana da cewa Adamun ya dauki nauyin wadannan dalibai.

Tun a yammacin jiya ne dai labaran yake ta yawo a sohiyal midiya na cewa a damun ya dauki nauyin karatun daliban inda wasu ke ta gasgata labarin wasu kuma ke karyatawa.

RUBUTU MASU ALAKA:

A saukakawa matasa lefe- inji Malama Ladi

Abinda ya sanya jaruma Barauniya rushewa da kuka

Kotu ta bada belin sadiya Haruna

Nishadi

Rayuwa ta ba ta da wata ma’ana a yanzu — Wizkid

Published

on

Guda daga cikin fitattun mawakan nan na Afrobeats, Ayodeji Balogun, wanda aka fi sani da Wizkid, ya bayyana cewa rayuwa ba ta da wata ma’ana a gare shi tun bayan mutuwar mahaifiyarsa, Misis Jane Dolapo Balogun.

Mawaki Wizkid ya bayyana halin da ya ke ciki a kafafen sada zumunta tun bayan mutuwar ta ta, inda ya ce rayuwarsa sam babu dadi bayan mutuwar mahaifiyar tasa.

Ta cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Instagram a ranar Laraba, mawakin ya bukaci masoyansa da su bi Ubangiji.

Jaridae Daily Trust ta ruwaito yadda mawakin ya rasa mahaifiyarsa a watan Agustan 2023, a lokacin da yake kan bulaguron wakokin sabon kundin wakarsa mai suna ‘More Love Less Ego’ a Turai.

Ya rubuta, “Kwanaki bayan na rasa mahaifiyata; Rayuwa ba ta da ma’ana! Amma mun ji. Wani lokaci dole ne ku bar komai ya tafi. A bi Ubangiji kawai, “A cewarsa”.

Rahotanni sun bayyana cewa a ranar Talata, Wizkid ya tayar da hankula a tsakanin magoya bayansa, bayan da ya wallafa hoton sa yana gadon asibiti a shafinsa na Instagram a cikin wani yanayi.

A cikin hoton dai mawakin ya yi nuni da cewar za’a duba shi, amma bai bayyana mai yake samunsa ba, lamarin da ya haifar da cece-kuce a shafun na sada zumunta.

Continue Reading

Nishadi

Na yi asarar dala biliyan 2 a rana ɗaya kuma har yanzu ina raye – Mawakin Amurka

Published

on

Ba’amurke kuma mawaki, Kanye Omari West, wanda aka fi sani da Kanye West ko Ye, ya yi asarar dala biliyan 2 a cikin sa’o’i 24, bayan wasu kamfanoni da dama sun yanke alaka da shi saboda kalaman kyamar Yahudawa.

Wannan na zuwa ne kasa da sa’o’i 48, bayan wata mujallar kasuwanci ta Amurka, Forbes, ta sanar da cewa Kanye ba shi da wani matsayi a cikin jerin masu kudi a yanzu bayan da yarjejeniyarsa mai tsoka da Adidas ta yanke hulda da shi.

Kamfanonin da suka yanke alaƙa da Kanye ya zuwa yanzu sun haɗa da Balenciaga, MRC (dakin nishaɗin da aka riga aka gama Ye Documentary), hukumar baiwar sa CAA, Adidas, Jaylen Brown da Aaron Donald, Foot Locker, The RealReal, T.J. Maxx, Madame Tussauds.

Da yake mayar da martani kan asarar, mawakin, a wani sako da ya wallafa a shafin Instagram, ya bayyana cewa mutanen shi ne, ba kudin ba.

Ya rubuta, “Na yi asarar dala biliyan 2 a rana ɗaya, kuma har yanzu ina raye. Wannan maganar soyayya ce, har yanzu ina son ku; kudin ba ni ba ne, jama’a su ne ni.”

Har ila yau, makarantarsa, Donda Academy, abun ya shafa ta, yayin da aka fitar da su daga gasar makarantar sakandare saboda maganganun Kanye.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

Magen gidan Firaministar Birtaniya na dakon uwar dakin ta

Published

on

A yau ne iyalan tsohon firaministan Burtaniya Boris Johnson ke tattara komatsansu a shirye-shiryen da suke yi na bankwana da gidan firaministan wanda ke Downing Street, domin bayar da waje ga sabuwar firaministar Mrs Liz Truss tare da iyalanta, wacce za ta ci gaba da zama a gidan na tsawon mulkinta,

To sai dai yayin da ake wannan shiri na ficewa daga gidan Kyanwar gidan mai suna ‘Lary’ na nan daram a gidan tana jiran isowar sabuwar firaministar

A rahoton BBC sun ce, Lary wacce ba mallakin kowa ba ce, ta zama babbar Kyanwar gidan firaminstan Birtaniya.

Kyanwar mai shekara 15, wacce ta yi zamani da firaministocin Burtaniya har guda uku, na shirin zama da iyalan Mrs Truss.

Continue Reading

Trending