Nishadi
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su

Mahukunta a makarantar Farfesa Ango Abdullahi dake Zaria, sun tabbatar da cewa jarumin fina-finan Hausa Adam A. Zango ya dauki nauyin karatun dalibai marayu guda 101 a makarantar.
Yayin tattaunawar da Dala FM tayi da shugaban makarantar Mallam Hamza Jibril ya tabbatar mana da cewa sun samu takarda daga dauke da bayanan cewa Adam Zango yana son zai dauki nauyin karatun dalibai har guda 101, kuma bayan da suka gama tattaunawa tuni Adam Zangon ya biya kudin tun a makon da ya gabata.
Hotunan takardun shaidar biyan kudin da Adam Zango yayi.
Dangane da daliban da za’a dauki nauyin karatun nas Mallam Hamza ya bayyana cewa Adam Zango ya baiwa masarautar Zazzau gurbin mutane 50 sai jam’iyyar APC aka bata gurbin mutane 31 sai kuma jam’iyyar PDP da aka baiwa mutane 20.
Dukkan su bisa sharadin zasu kawo dalibai marayu, ko talakawa da iyayen su basu da ikon biya musu kudin makaranta.
Haka zalika Mallam Hamza ya karyata dukkan rahotonnin dake yawo a soshiyal midiya na cewa batun daukar nauyin karya ne ba gaskiya bane.
Duk kokarin da Dala FM tayi na jin ta bakin jarumin Adam A. Zango amma abin ya ci tura, sai dai wani makusancinsa ya tabbatar mana da cewa Adamun ya dauki nauyin wadannan dalibai.
Tun a yammacin jiya ne dai labaran yake ta yawo a sohiyal midiya na cewa a damun ya dauki nauyin karatun daliban inda wasu ke ta gasgata labarin wasu kuma ke karyatawa.
RUBUTU MASU ALAKA:
A saukakawa matasa lefe- inji Malama Ladi
Abinda ya sanya jaruma Barauniya rushewa da kuka
Kotu ta bada belin sadiya Haruna

Nishadi
Na yi asarar dala biliyan 2 a rana ɗaya kuma har yanzu ina raye – Mawakin Amurka

Ba’amurke kuma mawaki, Kanye Omari West, wanda aka fi sani da Kanye West ko Ye, ya yi asarar dala biliyan 2 a cikin sa’o’i 24, bayan wasu kamfanoni da dama sun yanke alaka da shi saboda kalaman kyamar Yahudawa.
Wannan na zuwa ne kasa da sa’o’i 48, bayan wata mujallar kasuwanci ta Amurka, Forbes, ta sanar da cewa Kanye ba shi da wani matsayi a cikin jerin masu kudi a yanzu bayan da yarjejeniyarsa mai tsoka da Adidas ta yanke hulda da shi.
Kamfanonin da suka yanke alaƙa da Kanye ya zuwa yanzu sun haɗa da Balenciaga, MRC (dakin nishaɗin da aka riga aka gama Ye Documentary), hukumar baiwar sa CAA, Adidas, Jaylen Brown da Aaron Donald, Foot Locker, The RealReal, T.J. Maxx, Madame Tussauds.
Da yake mayar da martani kan asarar, mawakin, a wani sako da ya wallafa a shafin Instagram, ya bayyana cewa mutanen shi ne, ba kudin ba.
Ya rubuta, “Na yi asarar dala biliyan 2 a rana ɗaya, kuma har yanzu ina raye. Wannan maganar soyayya ce, har yanzu ina son ku; kudin ba ni ba ne, jama’a su ne ni.”
Har ila yau, makarantarsa, Donda Academy, abun ya shafa ta, yayin da aka fitar da su daga gasar makarantar sakandare saboda maganganun Kanye.

Ƙasashen Ƙetare
Magen gidan Firaministar Birtaniya na dakon uwar dakin ta

A yau ne iyalan tsohon firaministan Burtaniya Boris Johnson ke tattara komatsansu a shirye-shiryen da suke yi na bankwana da gidan firaministan wanda ke Downing Street, domin bayar da waje ga sabuwar firaministar Mrs Liz Truss tare da iyalanta, wacce za ta ci gaba da zama a gidan na tsawon mulkinta,
To sai dai yayin da ake wannan shiri na ficewa daga gidan Kyanwar gidan mai suna ‘Lary’ na nan daram a gidan tana jiran isowar sabuwar firaministar
A rahoton BBC sun ce, Lary wacce ba mallakin kowa ba ce, ta zama babbar Kyanwar gidan firaminstan Birtaniya.
Kyanwar mai shekara 15, wacce ta yi zamani da firaministocin Burtaniya har guda uku, na shirin zama da iyalan Mrs Truss.

Labarai
Na saka takalmi Sneakers da shirin ko ta kwana – Kashim Shettima

Mataimakin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Kashim Shettima, ya mayar da martani kan sukar sa da aka yi masa a lokacin da ya halarci taron kungiyar lauyoyin ta kasa NBA a jihar Legas.
Hotunan Shettima dai sun yi ta yawo a dukkanin kafafen sada zumunta na zamani, wanda aka caccake shi a kan takalmin da ya saka da rigar Kwat.
Sai dai Shettima, a cikin wani faifan bidiyo da yake zagayawa a halin yanzu, ya bayyana cewa da gangan ya sanya takalmin sneakers a wajen taron wanda ya gudana a ranar Litinin.
Ya ce ya sanya sneakers ne a wajen taron, saboda akwai wani shiri da dan takarar shugaban kasa da magoya bayansa suka yi nayin barna a wurin taron.
A cewar Shettima, “Daya daga cikin ‘yan takarar shugaban kasa, tawagarsa sun gudanar da tarurruka na tsawon kwanaki uku a jere, wanda hakan za su iya tayar da rikici a wajen, lokacin da aka ce min jama’a ne masu adawa. Ni ma’aikacin banki ne, wanda ɗayan manyan ma’aikatan banki ne a duniya ya horar da ni. Ni ɗan Jim Ovia ne. Da gangan na sanya sneakers zuwa taron NBA don yin izgili a kansu. “

-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Manyan Labarai4 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai3 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi4 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai4 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya1 year ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai4 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Manyan Labarai4 years ago
Ba’amurkiya da masoyin ta sun hada cinkoso a kasuwar Sabon Gari