Connect with us

Rahotonni

Me kuka sani game da shari’ar musulunci a Najeriya?

Published

on

Malamai da mabiya addinin musulunci a jihohin Arewacin kasar nan sun dauki tsawon lokaci suna fafutukar ganin an kafa shari’ar musulunci a sassa daban-daban na kasar.

Biyo bayan kiraye-kiraye na mabiya addinin musulunci ya sanya gwamnan jihar Zamfara a wancan lokacin Ahmad Sani Yariman Bakura ya sanar da cewa jihar Zamfara zata fara aiki da tsari irin na shari’ar addinin musulunci a ranar 27 ga watan Octoba na shekarar 1999.

Jihar Zamfara itace jiha ta farko da ta fara kaddamar da shari’ar musuluncin a ranar 27 ga watan Janairu na shekara ta 2000, sai jihar Kano dake biye mata baya inda gwamnan jihar na wancan lokaci Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso ya kaddamar da shari’ar a watan 6 na shekara ta 2000.

Jihar Sokoto da kuma jihar Katsina sun biyewa jihar Kano baya inda suma suka kaddamar da tsarin shari’ar musulunci a karshen shekarar ta 2000.

Jihohin Bauchi, Borno, Jigawa, Kebbi da kuma jihar Yobe suma sun bi sahun sauran jihohin da suka kaddamar da shari’ar tun da farko a shekarar 2001.

Su kuwa jihohin Kaduna, Niger da kuma jihar Gombe sun kaddamar da shari’ar musulunci ne a wasu sassa na jihohinsu da musulmai ke da rinjaye, kasancewar suna da al’umma da dama masu mabam-bamta addini a jihar.

Al’ummar musulmi dai sunyi farin ciki matuka da kaddamar da shari’ar a wancan lokaci.

RUBUTU MASU ALAKA:

An sauke masu rike da mukamai a Hisbah

Munyi hannun riga da rashawa- Hisba

Hisbah ta bukaci maza da su dinga barin kananan ‘ya’yansu a wajen iyaye mata idan an samu rabuwar aure

Labarai

Za mu daƙile tayar da hargitsi yayin yanke hukuncin zaɓen gwamna- Civil Defence

Published

on

Rundunar tsaro da bayar da kariya ga al’umma ta Civil Defence da ke jihar Kano, ta ce, za ta gudanar da aikin ba sani ba sabo a kan dukkanin waɗanda suka nemi tayar da hargitsi a gobe Laraba, yayin yanke hukuncin zaɓen gwamna a jihar.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar DSC Ibrahim Idris Abdullahi ne, ya bayyana hakan, yayin zantawarsa da gidan rediyon Dala FM a ranar Laraba, lokacin da yake tsokaci kan haɗin kan da za su yi da sauran rukunin jami’an tsaro kan tsaron da za su bayar yayin yanke hukuncin da Kotun karɓar ƙorafe-korafen zaɓen gwamna za tayi a gobe Laraba.

Ya ce, “Ba za su saurarawa duk wanda ya nemi tayar da hargitsin ba”.

Wakilnmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewar, DSC Ibrahim Idris ya kuma yi kira ga shugabannin al’umma, da su ka haɗar da masu riƙe da masarautun gargajiya, malamai da sauransu da su ci gaba da wayar da kan mutane domin ganin an samu zaman lafiya da cigaba.

Continue Reading

Labarai

Za mu bai wa ɗaurarru aikin koyarwa – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce, za ta bawa ɗaurarrun da suka kammala karatu aikin koyarwa, domin bunƙasa ilimin su.

Kwamishinan ilmin jihar, Umar Haruna Doguwa ya bayyana hakan, lokacin bikin ta ya murna ga daliban 48 da suka kammala karatun sakandare, a makarantar Iinmate continue education center da ke gidan gyaran hali na Kurmawa a nan Kano.

Ya ce, nan ba da dadewa ba, gwamnati za ta samar da kwamitin yiwa daurarru afuwa, wanda a ciki in dai akwai waɗanda suka cancanta za su iya samun aikin.

Daga bisani kwamishinan ya yi alkawarin bada kowacce irin gudunmawar gwamnati, domin tallafar harkar koyo da koyarwar gidan gyaran halin.

A nasa jawabin, shugaban gidajen ajiya da gyaran hali na jihar Kano, Sulaiman Muhammad Inuwa, ya ce, akwai buƙatar gwamnati da masu hannu da shuni su taimaka wa harkar karatun gidan gyaran halin, domin ganin an sami al’umma ta gari.

Continue Reading

Labarai

Mu taimaka wa masu ƙaramin ƙarfi domin rage musu raɗaɗin rayuwa – Ambada Muhammad

Published

on

Shugaban ƙungiyar mu haɗa zumunci ta KHZ Foundation dake nan Kano Ambasada Dakta Muhammad Abdulsalam, ya ce, taimakawa masu ƙaramin ƙarfi musamman a wannan lokaci na watan Azumin Ramadana, zai taimaka musu wajen rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Ambasada Muhammad Abdulsalam ya bayyana hakan ne a yayin taron baiwa iyayen marayu da masu ƙaramin ƙarfi tallafin kayan abinci a ofishin kungiyar yau Litinin, da kuma basu a wasu unguwanni da suka haɗar da Tukuntawa da Sabuwar Gandu, Tinshama da dai sauransu.

Ya kuma ce, kamata yayi al’umma su ƙara himma wajen shiga makamancin ƙungiyar su domin baiwa al’umma gudunmawar da ta kamata, ta hanyoyi daban-daban, domin cire musu wata damuwa da ta damesu a rayuwa.

“Zamu fitar da ɗaurarru masu ƙananan tara a wasu gidjen ajiya da gyaran hali domin fitar da su daga halin rayuwar da suke ciki na jarrabta da suka tsinci kan su”. In ji Ambasada Muhammad.

Da yake nasa jawabin malami a kwalejin ilmin tarayya ta FCE dake nan Kano Mallam Ibrahim Muhammad Gandu, gargaɗar iyayen marayun da sukaci gajiyar tallafin yayi, da su yi amfani da kayayyakin abincin ta hanyar da ta dace Mai-makon siyar da kayan a ƙasƙance da ake zargin wasu suna yi a wasu lokutan.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewar, iyayen marayu da masu ƙaramin ƙarfi da dama ne suka rinƙa bayyana farin cikinsu, bisa basu kayan abincin da akayi, wanda suka haɗar da Shinkafa, Gero Taliya Man girki da sai sauransu, haɗi da Naira dubu ɗaya kuɗin Mota ga kowannen su.

Continue Reading

Trending