Connect with us

Labarai

Dan KAROTA ya gamu da Ajalin sa

Published

on

Kakakin rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano DSP Abdullahi Haruna Kyawa ya tabbatar da cewa wani Jami’in hukumar karota ya gamu da ajalinsa ana Kano.

DSP Abdullahi Haruna Kyawa ya ce dan KAROTAr ya gamu da ajalin sa ne alokacin da yake kokarin  kama wani mai karamar mota da ake zargin ya saba dokar titi a yankin Yan Dusa, dake dakata a nan Birnin Kano.

Haruna Kiyawa ya ce tabbas sun sami labarin yayin da tuni suka fara tattara bayanai kan wannan batun.

Rahotannin sun bayyana cewar ana dai zargin mai karamar motar ya bi ta kan ruwan cikin jami’in hukumar KAROTA ya kuma tsere.

haha zalika Marigayin wanda ake kira da Tijjani Adamu na aiki ne a sashin ayyukan yau da kulluma na hukumar KAROTA yayin da ya gamu da iftala’in rasa ran sa.

wakilin mu Abba Isa Muhammad ya rawaito cewar,dan KAROTAR na tsaka da gudanar da aikin sa a lokacin da ya gamu da  iftila’in sa na rasa ran sa.

Abba Isa ya ce jami’an KAROTA sun sheda masa cewar, mai karamin motar ya nemi jami’in su da ya sake shi amma yaki amincewa da bukatar sa a don haka ya dauki matakin bin ta kan sa.

Haka zalika kakakin hukumar KAROTA ta jihar Kano Nabulusi Abubakar Kofar Na’isa yace tuni hukumar ta dauki gawar ta mika ga jami’an ‘yan sanda kuma tuni aka mikata dakin ajiye gawarwaki na Asibitin Kwararru na Murtala.

 

 

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Trending