Connect with us

Lafiya

Yanzu- Yanzu: Ganduje ya fitar da sunayen kwamishinoni

Published

on

Gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya aike da sunayen mutum 20 zuwa majalisar dokoki domin tantance su don tabbatar da su a matsayin Kwamishinoni.

Kakakin Majalisar Abdu’aziz Garba Gafasa ne ya bayyana sunayen a cikin kwaryar majalisar lokacin zaman majalisar.

Da safiyar yau ne majalisar ta zauna don sauraran sunayen da gwamnan ya aike mata.

Da ya ke karanta wasikar da gwamnan ya turowa majalisar da safiyar yau, shugaban majalisar dokokin ta Kano Abdul Aziz Garba Gafasa ya ce, wadanda gwamnan ya turo da sunayensu don nadasu a matsayin kwamishinonin sun hada da: Murtala Sule Garo, Eng Muhd Mu’azu Magaji, Barrister Ibrahim Mukhtar, Musa Ilyasu Kwankwaso, Dr Kabiru Ibrahim Getso, Comrade Muhd Garba, Nura Muhd Dankade, Shehu NaAllah Kura.

Dr. Muhd Tahar Adam,  Dr. Zubairu Umar Muhd, Dr Aminu Ibrahim Tsanyawa, Sadiq Aminu Wali, Muhd Baffa Takai, Kabiru Ado Lakwaya, Dr Mariya Mahmud Bunkure, Ibrahim Ahmad Karaye, Mukhtar Ishaq Yakasai, Mahmud Muhd Dantsantsi, Muhd Sunusi Said Kiru, Barrister Lawan Abdullahi Musa.

Sauran sune Kabiru Ado Lakwaya da Dr Aminu Ibrahim Tsanyawa da Barrister Ibrahim Muktar da kuma Eng Mu’azu Magaji.

Wakiliyar mu ta majalisa Khadija Ishaq ta rawaito cewa  ya ruwaito cewa a gobe talata ne ake sa ran fara tantance su.

 

Lafiya

Ku rinƙa ziyartar Asibiti ana muku gwaje-gwajen fitsari da Jini domin sanin halin da ƙodar ku take ciki – Likita

Published

on

An shawarci al’umma da su rinƙa ziyartar Asibiti akai akai wajen duba lafiyar su, ta hanyar yin gwaje-gwajen fitsari da jini domin sanin halin da kodar su ke ciki.

Dakta Muhajid Sunusi Rabi’u ne ya bayyyana hakan yayin ganawarsa da Dala FM, lokacin da suke aikin gwaje-gwajen fitsari da jini, kyauta a ɗaya daga cikin makarantu masu zaman kan su a nan Kano.

Dakta Mujaheed ya kuma ce sun gudanar da aikin ne a wani ɓangare na bikin ranar ƙoda ta Duniya, wadda aka ware duk ranar Alhamis ta mako na biyu na kowanne watan Maris domin gudanar da bikin ranar.

Continue Reading

Lafiya

Za’a yiwa kusan yara miliyan 3 rigakafin cutar shan Inna a Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano tace kusan Yara miliyan 3 za’ayiwa rigakafin cutar shan inna a kananan hukumomin jihar nan 44, duba da samun ɓurɓushinta da kaso 65, a jihar ta Kano.

Kwamishinan lafiya na jihar Kano Dakta Abubakar Labaran Yusuf ne ya bayyana hakan yayin ƙaddamar da rigakafin cutar shan innar a yau Alhamis, wanda za’a kwashe kwanaki 4 ana gudanarwa a Kano.

Dakta Abubakar Labaran ya ce duba da shigowar zafin akwai buƙatar al’umma su kula da alamomin cutar sankarau, duk da gwamnati ta yi shirin bayar da agajin gaggawa, kamar yadda tashar Dala FM Kano ta rawaito.

Ma’aikatar lafiyar ta jihar Kano dai ta ce za’a ci gaba da gudanar da sauran rigafin, domin bai wa yaran jihar Kano kariya daga cututtuka masu yaɗuwa.

Continue Reading

Lafiya

Dokar tilasta gwajin lafiya kafin aure ta tsallake karatu na biyu a majalisar dokokin Kano

Published

on

Rahotanni na bayyana cewar majalisar dokokin jihar Kano, ta yi karatu na biyu a kan kudirin dokar tilasta wa masu niyyar yin aure yin gwajin cutar kanjamau, da na cutar hanta da kuma duba kwayoyin jini wato Sikila, gabanin daura aure.

Ɗan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Takai, Hon.Musa Ali Kachako, shin wanda ya kawo kudirin dokar, ya bayyana cewa, jihar Kano na fama da matsalolin lafiya daban-daban da suka hada da cutar kanjamau saboda mutane kan yi aure ba tare da an duba lafiyarsu ba, hakan ne ma ya sa ya kai ƙudirin.

Kachako, ya ce, ƙudirin dokar idan har aka amince da shi, zai ceci rayuka da dama tare da dakile yaɗuwar cututtuka masu barazana ga rayuwar al’umma, kamar yadda jaridar Kadaura24 ta rawaito.

Da yake nuna goyon bayansa kan ƙudirin Ɗan majalisa Hon. Aminu Sa’ad, mamba mai wakiltar mazabar Ungogo, ya ce, jihohin Jigawa, Katsina da Kaduna sun zartar da irin wannan kudiri domin magance kalubalen kiwon lafiya da suke fuskanta.

Ya ce tilas ne Kano da ke da yawan al’umma a kasar nan ta zartar da kudirin dokar, domin kare lafiyar ‘yan jiharta ta hanyar samar da gwaje-gwaje kafin aure domin dakile yaduwar cututtuka, kamar cutar hanta, da sauran cututtuka.

Continue Reading

Trending