Connect with us

Labarai

Dambarwa ta barke tsakanin KEDCO da mutanen unguwar Shagari Quaters

Published

on

Biyo bayan shafe tsawon kwanaki 22 babu wutar lantarki a unguwar Shagari Quarters dake nan Kano, al’ummar yankin sun kai karar kamfanin rarraba wutar lantarki na Kano KEDCO ga hukumar karbar korafe-korafe ta kasa Nigerian Regulatory Commission.

Tun da farko dai kamfanin KEDCO ya nemi al’ummar unguwar da su samar da turakun lantarki don kaucewa biyowar wayoyin wutar lantarki ta cikin gidajen su, sai dai al’ummar unguwar basu aminta da hakan ba, inda suka ce sai dai kamfanin na KEDCO ya saka musu turakun.

Hukumar karbar korafe-korafen tayi zama na musamman domin kawo dai-daito a tsakanin bangarorin, inda aka cimma matsaya cewa al’ummar zasu fara yin karo-karo a tsakanin su domin a cike gurbin turakun lantarkin.

A bangaren kamfanin KEDCO kuwa ya ce ba zai dawo musu da wutar ba har sai sun kammala samar da turakun, saboda hatsarin da za’a iya samu in suka sako wuta zuwa unguwar.

Sai dai al’ummar unguwar sunyi zargin cewa akwai wani layi guda daya da yake da wutar lantarki, bayan an yanke wutar duka unguwar, sai dai jami’an KEDCO basu bada amsar wannan tambayar ba.

Al’ummar unguwar Shagari Quarters dai sun bayyana cewa layin dake da wutar lantarkin layin gidan surukar shugaban kamfanin KEDCO ne.

Rubutu masu alaka:

An gargadi KEDCO kan magance korafe-korafen jama’a

Zamu dauke lantarki a jihohin Kano Katsina da Jigawa- KEDCO.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending