Connect with us

Nishadi

Kanyywood: Anyi bikin jaruma Hafsat Shehu

Published

on

A ranar jumu’ar da ta gabata ne aka daura Auren fitacciyar jarumar nan wato Hafsat Shehu, a nan Kano, wadda tsohuwar matar fitaccen jarumin nan ne marigayi Ahmad S. Nuhu, wanda shi ne mijinta na farko.

Marigayi Ahmad S. Nuhu da Hafsat Shehu a shekarun baya.

Bayan rasuwar jarumin Hafsat Shehu tayi aure a birnin tarayya Abuja, sai dai auren bai jima aka samu rabuwa.

Tun bayan wancan lokacin jarumar tayi kokarin dawowa masana’antar Kannywood amma abin bai yiwu ba, saidai a baya-bayan nan daya daga manyan jaruman masana’antar Adam A. Zango ya sanya ta acikin wani Film dinsa mai suna Basaja Sabon Labari, sai dai har izuwa yanzu ba’a kai ga fara daukar film din ba.

Jaruma Hafsat Shehu dai tayi irin Auren nan da mafi yawa jarumai mata na Kannywood keyi wato a boye Ango, sannan a boye ranar Aure sai ga iya ‘yan uwa da abokanan arziki na kusa, domin kuwa kawai sai gani aka yi wasu jaruman na ta wallafa mata sakonnin Allah ya bada zaman lafiya.

Waiwaye:

An haifi jaruma Hafsat Shehu ne a ranar 28 ga watan Nuwamba shekara ta 1976 yayin da shi kuma marigayi Ahmad S. Nuhu mijinta na farko aka haife shi a ranar 15 ga watan Fabrairu na shekarar 1976.

Jarumar ta bada gudunmuwa sosai a fina-finan hausa a shekarun baya, kuma mafi yawan fina-finanta tana taka rawa ne tare da marigayin wato Ahmad S. Nuhu, inda daga bisani soyayya ta kullu har ta kai su ga yin Aure.

Manazarta fina-finan Hausa na kallon ba’a taba samun wata soyayya mai karko tsakanin jaruman masana’antar ba kamar ta marigayi Ahmad S. Nuhu da Hafsat Shehu.

Kalli wasu hotunan jaruman a kasa:

Muna fatan Allah ya gafartawa marigayin, Amarya kuma Allah ya bada zaman lafiya.

Rubutu masu alaka:

Jamila Nagudu ce ta can-canta da zama gwarzuwar Kannywood –Kamaye

Jarumi Madagwal na fama da rashin lafiya

Labarai

Kannywood:- MOPAN za ta fara raba ID CARD

Published

on

Hadaddiyar kungiyar masu shirya fina-finai ta Mopan na sanar da dukkanin wadanda sukayi rijista cewa za ta fara bayar da shaida wato ID CARD ga masu bayar da umarni, da masu shirya fina-finai da masu daukar hoto me motsi cewa za’a fara basu ID CARD daga ranar 25 ga wannan wata.

 

Cikin sanarwa da shugaban kungiyar na kano Ado Ahmad Gidan Dabino ya fitar, ya ce bayar da ID CARD din ya shafi iya wadanda aka ambata ne kadai banda jarumai.

 

A cewar sa shaidar su ma Jarumai za’a fara bayar da nasu da zarar an kammala tantance su.

 

A don haka ƙungiyar ta MOPPAN ke sanar da dukkanin wadanda aka ambata da su ka tabbatar sunyi rijista da su je ofishin kungiyar domin karbar ID CARD.

Continue Reading

Nishadi

Rayuwa ta ba ta da wata ma’ana a yanzu — Wizkid

Published

on

Guda daga cikin fitattun mawakan nan na Afrobeats, Ayodeji Balogun, wanda aka fi sani da Wizkid, ya bayyana cewa rayuwa ba ta da wata ma’ana a gare shi tun bayan mutuwar mahaifiyarsa, Misis Jane Dolapo Balogun.

Mawaki Wizkid ya bayyana halin da ya ke ciki a kafafen sada zumunta tun bayan mutuwar ta ta, inda ya ce rayuwarsa sam babu dadi bayan mutuwar mahaifiyar tasa.

Ta cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Instagram a ranar Laraba, mawakin ya bukaci masoyansa da su bi Ubangiji.

Jaridae Daily Trust ta ruwaito yadda mawakin ya rasa mahaifiyarsa a watan Agustan 2023, a lokacin da yake kan bulaguron wakokin sabon kundin wakarsa mai suna ‘More Love Less Ego’ a Turai.

Ya rubuta, “Kwanaki bayan na rasa mahaifiyata; Rayuwa ba ta da ma’ana! Amma mun ji. Wani lokaci dole ne ku bar komai ya tafi. A bi Ubangiji kawai, “A cewarsa”.

Rahotanni sun bayyana cewa a ranar Talata, Wizkid ya tayar da hankula a tsakanin magoya bayansa, bayan da ya wallafa hoton sa yana gadon asibiti a shafinsa na Instagram a cikin wani yanayi.

A cikin hoton dai mawakin ya yi nuni da cewar za’a duba shi, amma bai bayyana mai yake samunsa ba, lamarin da ya haifar da cece-kuce a shafun na sada zumunta.

Continue Reading

Nishadi

Na yi asarar dala biliyan 2 a rana ɗaya kuma har yanzu ina raye – Mawakin Amurka

Published

on

Ba’amurke kuma mawaki, Kanye Omari West, wanda aka fi sani da Kanye West ko Ye, ya yi asarar dala biliyan 2 a cikin sa’o’i 24, bayan wasu kamfanoni da dama sun yanke alaka da shi saboda kalaman kyamar Yahudawa.

Wannan na zuwa ne kasa da sa’o’i 48, bayan wata mujallar kasuwanci ta Amurka, Forbes, ta sanar da cewa Kanye ba shi da wani matsayi a cikin jerin masu kudi a yanzu bayan da yarjejeniyarsa mai tsoka da Adidas ta yanke hulda da shi.

Kamfanonin da suka yanke alaƙa da Kanye ya zuwa yanzu sun haɗa da Balenciaga, MRC (dakin nishaɗin da aka riga aka gama Ye Documentary), hukumar baiwar sa CAA, Adidas, Jaylen Brown da Aaron Donald, Foot Locker, The RealReal, T.J. Maxx, Madame Tussauds.

Da yake mayar da martani kan asarar, mawakin, a wani sako da ya wallafa a shafin Instagram, ya bayyana cewa mutanen shi ne, ba kudin ba.

Ya rubuta, “Na yi asarar dala biliyan 2 a rana ɗaya, kuma har yanzu ina raye. Wannan maganar soyayya ce, har yanzu ina son ku; kudin ba ni ba ne, jama’a su ne ni.”

Har ila yau, makarantarsa, Donda Academy, abun ya shafa ta, yayin da aka fitar da su daga gasar makarantar sakandare saboda maganganun Kanye.

Continue Reading

Trending