Connect with us

Rahotonni

‘Yan Soshiyal Midiya na neman a soke lefe

Published

on

Wani batu dake cigaba da jan zare a shafukan sada zumunta shine batun A Soke Lefe da masu amfani da shafukan ke ta kiraye-kiraye a kai, wanda ake ta tafka muhawara tsakanin samari da ‘yan mata.

Sai dai ‘yan mata na ta sukar wannan bukata, inda su ma suke ganin matukar za’a soke lefe to sai an hada da kayan daki.

Wannan dai ba sabon abu bane a wurin masu amfani da soshiyal midiya, domin kuwa sun saba tsokano sama da kara amma a iya shafukan, kafin mu waiwayo muku wasu daga batutuwan da ‘yan soshiyal midiya suka sha tafkawa, ku kalli yadda suke tafka cecekuce a yanzu kan kokarin su na ganin an soke lefe a kasa.









Waiwaye:

A shekara ta 2016 cecekuce da masu amfani da soshiyal midiya suka yi, ya tilastawa gwamnatin tarayya dakatar da shirinta na gina cibiyar shirya fina-finai a Kano wato Film Village.

Haka ma dai a shekarar 2018 da ta gabata, ‘yan soshiyal midiya sun bada gudummuwa matuka wajen ganin an ceto wata matashiya ‘yar jihar Kano mai suna Zainab Habib Aliyu wadda mahukunta suka tsare a kasar Saudia bisa zargin safarar miyagun kwayoyi.

Labarin matashin nan Yunusa Yellow shi ma batu ne da ya nuna tasirin ‘yan soshiyal midiya a Arewacin Najeriya wanda yanzu haka mahukunta sun shiga cikin lamarin nan.

Na baya-bayan nan shi ne batun yaran Kano 10 da aka sace zuwa kudancin kasar nan inda ‘yan soshiyal midiya suka kirkiri wani Hashtag mai suna #Kano9 wanda yayi karfi sosai a shafin Twitter da Facebook da sauran shafukan intanet.

Irin wannan dai sun sha faruwa birjik, dukda cewa manazarta na ganin akwai tarin batutuwa marasa muhimmanci da masu amfani da soshiyal midiya keyi kamar labarin shugaba Buhari zai kara aure, ko na Aisha Buhari tayi yaji da makamantan su.

Abin jira dai a gani shi ne ko wane tasiri wannan yunkuri na Asoke Lefe zaiyi?

Rubutu masu alaka:

Kannywood: Kotu ta kori shari’ar Amina Amal

Jamila Nagudu ce ta can-canta da zama gwarzuwar Kannywood –Kamaye

Labarai

Za mu daƙile tayar da hargitsi yayin yanke hukuncin zaɓen gwamna- Civil Defence

Published

on

Rundunar tsaro da bayar da kariya ga al’umma ta Civil Defence da ke jihar Kano, ta ce, za ta gudanar da aikin ba sani ba sabo a kan dukkanin waɗanda suka nemi tayar da hargitsi a gobe Laraba, yayin yanke hukuncin zaɓen gwamna a jihar.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar DSC Ibrahim Idris Abdullahi ne, ya bayyana hakan, yayin zantawarsa da gidan rediyon Dala FM a ranar Laraba, lokacin da yake tsokaci kan haɗin kan da za su yi da sauran rukunin jami’an tsaro kan tsaron da za su bayar yayin yanke hukuncin da Kotun karɓar ƙorafe-korafen zaɓen gwamna za tayi a gobe Laraba.

Ya ce, “Ba za su saurarawa duk wanda ya nemi tayar da hargitsin ba”.

Wakilnmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewar, DSC Ibrahim Idris ya kuma yi kira ga shugabannin al’umma, da su ka haɗar da masu riƙe da masarautun gargajiya, malamai da sauransu da su ci gaba da wayar da kan mutane domin ganin an samu zaman lafiya da cigaba.

Continue Reading

Labarai

Za mu bai wa ɗaurarru aikin koyarwa – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce, za ta bawa ɗaurarrun da suka kammala karatu aikin koyarwa, domin bunƙasa ilimin su.

Kwamishinan ilmin jihar, Umar Haruna Doguwa ya bayyana hakan, lokacin bikin ta ya murna ga daliban 48 da suka kammala karatun sakandare, a makarantar Iinmate continue education center da ke gidan gyaran hali na Kurmawa a nan Kano.

Ya ce, nan ba da dadewa ba, gwamnati za ta samar da kwamitin yiwa daurarru afuwa, wanda a ciki in dai akwai waɗanda suka cancanta za su iya samun aikin.

Daga bisani kwamishinan ya yi alkawarin bada kowacce irin gudunmawar gwamnati, domin tallafar harkar koyo da koyarwar gidan gyaran halin.

A nasa jawabin, shugaban gidajen ajiya da gyaran hali na jihar Kano, Sulaiman Muhammad Inuwa, ya ce, akwai buƙatar gwamnati da masu hannu da shuni su taimaka wa harkar karatun gidan gyaran halin, domin ganin an sami al’umma ta gari.

Continue Reading

Labarai

Mu taimaka wa masu ƙaramin ƙarfi domin rage musu raɗaɗin rayuwa – Ambada Muhammad

Published

on

Shugaban ƙungiyar mu haɗa zumunci ta KHZ Foundation dake nan Kano Ambasada Dakta Muhammad Abdulsalam, ya ce, taimakawa masu ƙaramin ƙarfi musamman a wannan lokaci na watan Azumin Ramadana, zai taimaka musu wajen rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Ambasada Muhammad Abdulsalam ya bayyana hakan ne a yayin taron baiwa iyayen marayu da masu ƙaramin ƙarfi tallafin kayan abinci a ofishin kungiyar yau Litinin, da kuma basu a wasu unguwanni da suka haɗar da Tukuntawa da Sabuwar Gandu, Tinshama da dai sauransu.

Ya kuma ce, kamata yayi al’umma su ƙara himma wajen shiga makamancin ƙungiyar su domin baiwa al’umma gudunmawar da ta kamata, ta hanyoyi daban-daban, domin cire musu wata damuwa da ta damesu a rayuwa.

“Zamu fitar da ɗaurarru masu ƙananan tara a wasu gidjen ajiya da gyaran hali domin fitar da su daga halin rayuwar da suke ciki na jarrabta da suka tsinci kan su”. In ji Ambasada Muhammad.

Da yake nasa jawabin malami a kwalejin ilmin tarayya ta FCE dake nan Kano Mallam Ibrahim Muhammad Gandu, gargaɗar iyayen marayun da sukaci gajiyar tallafin yayi, da su yi amfani da kayayyakin abincin ta hanyar da ta dace Mai-makon siyar da kayan a ƙasƙance da ake zargin wasu suna yi a wasu lokutan.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewar, iyayen marayu da masu ƙaramin ƙarfi da dama ne suka rinƙa bayyana farin cikinsu, bisa basu kayan abincin da akayi, wanda suka haɗar da Shinkafa, Gero Taliya Man girki da sai sauransu, haɗi da Naira dubu ɗaya kuɗin Mota ga kowannen su.

Continue Reading

Trending