Connect with us

Rahotonni

Al’umma na cigaba da raya daren Mauludi a Kano

Published

on

Al’ummar musulmi daga ko ina a fadin duniya na cigaba da gabatar da bukukuwan maludi domin murnar zagayowar ranar da aka haifi fiyayyen halitta manzon tsira Annabi (s.a.w), wanda ake yi duk shekara a wannan wata na Rabi’ul Auwal da muke ciki.

Haka abin yake a nan jihar Kano, inda tun kafin shigowar watan al’umma kama daga yara da manya, maza da mata ke ta shirya tarukan mauludi ba dare ba rana a sassa daban-daban na jihar Kano.

Ana kawata wurin Mauludi da kayan ado

Musulmi kan kawata wuraren taron Mauludi da ado kala-kala masu daukar hankali domin girmamawa ga Manzon Allah (s.a.w).

Me ake yi a taron Mauludi?

Musulmai na amfani da taron Mauludi wajen karantar da tarihin manzon tsira Annabi (s.a.w) da kuma koyar da ibadu bisa tsari da tarbiyyar addinin Musulunci.

Haka kuma akan rera kasidun bege, sannan akan baiwa dalibai karatuttuka wanda suke haddacewa su karanto a ranar Mauludi.

Al’umma na yin ankon kayan sawa na musamman domin ranar bikin, haka kuma akan yi girki kala-kala duka dai domin wannan biki.

Ana yin Mauludi ba dare ba rana a Kano

Al’umma na gudanar da bikin mauludi ba dare ba rana a birnin Kano, domin kuwa duk inda ka zaga a lungu da sako na jihar Kano zaka iske al’umma a sassa daban-daban na gudanar da bukuwan na Mauludi.

Gobe Lahadi shi ne dai-dai da ranar 12 ga watan Rabi’ul Auwal ta wannan shekarar, wato dai-dai da ranar da aka haifi fiyayyen halitta Annabi (s.a.w), wannan rana tana da matukar muhimmanci ga musulmi.

Labarai

Za mu daƙile tayar da hargitsi yayin yanke hukuncin zaɓen gwamna- Civil Defence

Published

on

Rundunar tsaro da bayar da kariya ga al’umma ta Civil Defence da ke jihar Kano, ta ce, za ta gudanar da aikin ba sani ba sabo a kan dukkanin waɗanda suka nemi tayar da hargitsi a gobe Laraba, yayin yanke hukuncin zaɓen gwamna a jihar.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar DSC Ibrahim Idris Abdullahi ne, ya bayyana hakan, yayin zantawarsa da gidan rediyon Dala FM a ranar Laraba, lokacin da yake tsokaci kan haɗin kan da za su yi da sauran rukunin jami’an tsaro kan tsaron da za su bayar yayin yanke hukuncin da Kotun karɓar ƙorafe-korafen zaɓen gwamna za tayi a gobe Laraba.

Ya ce, “Ba za su saurarawa duk wanda ya nemi tayar da hargitsin ba”.

Wakilnmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewar, DSC Ibrahim Idris ya kuma yi kira ga shugabannin al’umma, da su ka haɗar da masu riƙe da masarautun gargajiya, malamai da sauransu da su ci gaba da wayar da kan mutane domin ganin an samu zaman lafiya da cigaba.

Continue Reading

Labarai

Za mu bai wa ɗaurarru aikin koyarwa – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce, za ta bawa ɗaurarrun da suka kammala karatu aikin koyarwa, domin bunƙasa ilimin su.

Kwamishinan ilmin jihar, Umar Haruna Doguwa ya bayyana hakan, lokacin bikin ta ya murna ga daliban 48 da suka kammala karatun sakandare, a makarantar Iinmate continue education center da ke gidan gyaran hali na Kurmawa a nan Kano.

Ya ce, nan ba da dadewa ba, gwamnati za ta samar da kwamitin yiwa daurarru afuwa, wanda a ciki in dai akwai waɗanda suka cancanta za su iya samun aikin.

Daga bisani kwamishinan ya yi alkawarin bada kowacce irin gudunmawar gwamnati, domin tallafar harkar koyo da koyarwar gidan gyaran halin.

A nasa jawabin, shugaban gidajen ajiya da gyaran hali na jihar Kano, Sulaiman Muhammad Inuwa, ya ce, akwai buƙatar gwamnati da masu hannu da shuni su taimaka wa harkar karatun gidan gyaran halin, domin ganin an sami al’umma ta gari.

Continue Reading

Labarai

Mu taimaka wa masu ƙaramin ƙarfi domin rage musu raɗaɗin rayuwa – Ambada Muhammad

Published

on

Shugaban ƙungiyar mu haɗa zumunci ta KHZ Foundation dake nan Kano Ambasada Dakta Muhammad Abdulsalam, ya ce, taimakawa masu ƙaramin ƙarfi musamman a wannan lokaci na watan Azumin Ramadana, zai taimaka musu wajen rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Ambasada Muhammad Abdulsalam ya bayyana hakan ne a yayin taron baiwa iyayen marayu da masu ƙaramin ƙarfi tallafin kayan abinci a ofishin kungiyar yau Litinin, da kuma basu a wasu unguwanni da suka haɗar da Tukuntawa da Sabuwar Gandu, Tinshama da dai sauransu.

Ya kuma ce, kamata yayi al’umma su ƙara himma wajen shiga makamancin ƙungiyar su domin baiwa al’umma gudunmawar da ta kamata, ta hanyoyi daban-daban, domin cire musu wata damuwa da ta damesu a rayuwa.

“Zamu fitar da ɗaurarru masu ƙananan tara a wasu gidjen ajiya da gyaran hali domin fitar da su daga halin rayuwar da suke ciki na jarrabta da suka tsinci kan su”. In ji Ambasada Muhammad.

Da yake nasa jawabin malami a kwalejin ilmin tarayya ta FCE dake nan Kano Mallam Ibrahim Muhammad Gandu, gargaɗar iyayen marayun da sukaci gajiyar tallafin yayi, da su yi amfani da kayayyakin abincin ta hanyar da ta dace Mai-makon siyar da kayan a ƙasƙance da ake zargin wasu suna yi a wasu lokutan.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewar, iyayen marayu da masu ƙaramin ƙarfi da dama ne suka rinƙa bayyana farin cikinsu, bisa basu kayan abincin da akayi, wanda suka haɗar da Shinkafa, Gero Taliya Man girki da sai sauransu, haɗi da Naira dubu ɗaya kuɗin Mota ga kowannen su.

Continue Reading

Trending