Connect with us

Addini

Yadda ake gudanar da bikin Takutaha a Kano

Published

on

Haqiqa kowane irin al’amari, akwai yadda ake tsara shi kuma a gudanar da shi. Don haka, kowane irin biki a qasar Hausa akwai yadda ake gabatar da shi, wannan ya haxa da yadda ake tsattsara shi daki-daki da kuma irin dokokin da suke tafiyar da shi idan akwai. Bikin takutaha ya qunshi dukkan abubuwan da ake gabatarwa a wannan rana, kama daga karatuttuka da nuna murna ta hanyar nishadi da kuma ziyarce-ziyarcen ‘yan’uwa da abokan arziki.

Karanta: Kun san menene ma’anar  Takutaha?

Karatun Takutaha

A ranar takutaha haqiqa ana gabatar da karatuttuka daban-daban. Tun da sassafe malamai kan taru a cikin masallacin Madabo domin gabatar da wannan karatu. Daga cikin karatuttukan da ake gabatarwa akwai waqoqin yabon Annabi salallahu alaihi wasallam. Yawancin wannan waqoqi ana gabatar da su ne da harshen Larabci. Waqar da aka fi karantawa ita ce, Ishiriniya, sannan akwai kari na musamman wanda sai xan Madabo ne ya iya shi. Haka kuma, a cikin baitukan ishiriniyar, kowane gida a Madabo suna da baitinsu wanda suka zava suka nuna sha’awarsu a kai. Don haka, a duk lokacin da aka zo wannan baiti, akan yi wa shugaban wannan gidan addu’a don tunawa da shi (Hira da M.A.M,11-12-2008).

A duk lokacin da ake gabatar da karatun takutaha, ana ganin abubuwan ta’ajibi, domin akwai wani baiti na ishiriniya wanda da zarar an zo wurin, kowa yana miqewa tsaye, domin malamai sun ce, Manzon Allah salallahu alaihi wasallam yana halartar wurin. A wannan lokaci kuma, takardun ishiriniyar da ke hannun masu karatun, sukan tashi sama suna yawo a kan mutane. Haka kuma, makaru da ke jingine a masallacin kan rabu da qasa su zan yi sama (Hassan, 1998:95).

Hotunan wasu al’umma yayin bikin Takutaha na bana

Bayan karatun ishiriniya, ana gabatar da wasu waqoqin yabon Annabi salallahu alaihi wasallam cikin Larabci kamar haka:

Qasidar isma’uli

Isma’uni aqul                                      ya jami’i, ahlul aqul

Wa madahu hazar Rasul                                  haira min yamdahu Muhammad

Marhaba shahru atana                                   wulida fiha Nabina”

 

Fassarar Hausa

“ku saurare ni zan ambata                             ya jama’a ma’abota ambato

Yabon wannan Annabi                                               shi ne fiyayyen yabo na Annabi Muhammadu

Marhaba da watan da ya zo mana                 A cikinsa ne aka haifi Annabinmu”.

 

Qasidar Muqamul lada

Muqamul lada sudratul muntaha                    Li Ahmadu la shakka fi Mustapha

            Muqamun wa tallahi ma misluhu         Fa wahyun Ilaihi shadidil quwa

           

Lam kallamal Lahu Musa ala              Hamdan la shakka lil Mustapha

            Wa’inna Nabiyyin Abil Qasimu                        Habibur risalati fauqas sama

 

Fassarar Hausa

Muqami mafifici wato sudratul muntaha                     Ga Ahmadu babu shakka tare da Al-Mustapha

Wallahi babu wani muqami ya wannan                       wahayi ne daga Allah mai cikakken mulki.

 

Annabi Musa ya yi magana da Allah               godiya, babu shakka ga Al-Mustapha

Haqiqa Annabi baban Alqasim                                    Masoyin saqo daga Allah.

 

Qasidar Ahlan bi shahril Maulidi

          “Ahlan bi shahrul Maulidi                   Shahrul Nabiy Muhammadi

            Huwa bi sa’adil as’adi                        Khairil Wara Muhammadi”

 

Fassarar Hausa

Marhaba da watan Maulidi                 Watan Annabinmu Muhammadu

            Shi ne Mafificin masu xaukaka                        Mafi alhairin Al’umma Annabi Muhammadu”.

Sannan akwai sauran qasidu da dama kamar su: Qasidar iza raka’a zamanu da Rafa’atul Umuri da Asiru zunubi da Xanxarani da Shahrul rabi’i da sauransu.

Rubutu masu alaka:

Duk wanda ya tsere maka a kaunar manzo (s.a.w) ya tsere maka da komai –Limamin Jumu’a

Al’umma na cigaba da raya daren Mauludi a Kano

Marubuci: Tijjani Shehu Almajir

almajir02@yahoo.com

+234(0)8035943092

Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya,

Jami’ar Bayero, Kano.

Addini

Matsin Rayuwa: Shugabanni ku sassautawa al’umma – Babban Limamin Kano

Published

on

Babban limamin Kano, kuma wanda ya jagoranci sallar idi a babban masallacin idin na Kofar Mata a nan Kano, Farfesa Muhammed Sani Zaharaddin, ya ja hankalin shugabanni da su sassautawa al’umma, sakamakon halin matsin rayuwar da ake ciki a yanzu.

Farfesa Muhammed Sani Zaharaddin, yayi jan hankalin ne yayin huɗubar da ya gabatar, bayan kammala sallar idi da ta gudana a yau Laraba, a babban masallacin idin dake unguwar Kofar Mata a Kano.

Ya kara da cewa kasancewar al’umma na cikin mawuyacin hali da kuncin rayuwa, akwai buƙatar shugabanni su yi bakin ƙoƙarin su, domin kawo sauki daga halin matsin halin rayuwar da ake fama dashi.

Yayin sallar Idin gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, da mataimakin sa Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, da sauran al’umma da dama ne suka halarta.

Wakilinmu na fadar gwamnatin Kano Abba Haruna Idris ya rawaito cewa, Farfesa Muhammed Sani ya kuma ja hankalin al’umma, da su koma ga Allah Subhanahu wata’ala domin samun dacewa a Duniya da gobe Ƙiyama.

Continue Reading

Addini

Ku fara duban watan Sallah daga gobe Litinin – Fadar Sarkin Musulmi

Published

on

Yanzu haka kwamitin ganin wata na Fadar mai alfarma sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya buƙaci al’ummar musulmin ƙasar nan da su fara duban jinjirin watan Shawwal, daga gobe Litinin, 8 ga watan Afrilun, 2024 da ake ciki.

Bayanin hakan na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da kwamitin ya fitar a yammacin yau Lahadi a jihar Sokoto.

Sanarwar ta ce, duk wanda ya ga watan Shawwal, ya sanarwa Mai Gari ko Hakimi mafi kusa wanda kuma zai sanar har zuwa fadar Sarkin Musulmi.

Har ila yau, fadar Sarkin musulmin ta kuma bayar da lambobin waya waɗanda mutane za su yi amfani da su wajen ba da rahoton ganin watan Sallah ga fadar Sarkin musulmin, kamar yadda kafar yaɗa labarai ta BBC ta rawaito.

Continue Reading

Addini

Iyaye ku kula da tarbiyyar ƴaƴan ku – Malama Fatima Tsakuwa

Published

on

Malamar addinin musulunci dake nan Kano Malama Fatima Ahmad Tsakuwa, ta shawarci mata da su ƙara himma wajen kula da tarbiyyar ƴaƴansu, tare da kuma zaburar da su mahimmancin yin addu’a a cikin wannan wata na Ramadana, domin rabauta da rahamar Ubangiji S.W.T.

Malama Fatima Ahmad Tsakuwa, ta bayyana hakan ne yayin taron bita ta musamman da gidauniyar Bango Charity Foundation ƙarƙashin Malama Fatima Yusif Mai tama, wanda gidauniyar ta shirya wa Mata, da bitar ta shafi watan Azumin Ramadana, akan yadda iyaye matan za su kula da ƴaƴan su, da ya gudana a ofishin ƙungiyar dake unguwar Sharaɗa a Kano.

Wakiliyar tashar Dala FM Kano, ta rawaito cewa malama Fatima Tsakuwa ta ce akwai buƙatar iyayen su ƙara lura da tarbiyyar ƴaƴansu, tare da yawaita karatun Al-kur’ani mai girma domin rabauta da falala a wajen Allah S.W.T.

Continue Reading

Trending