Addini
Yadda ake gudanar da bikin Takutaha a Kano
Haqiqa kowane irin al’amari, akwai yadda ake tsara shi kuma a gudanar da shi. Don haka, kowane irin biki a qasar Hausa akwai yadda ake gabatar da shi, wannan ya haxa da yadda ake tsattsara shi daki-daki da kuma irin dokokin da suke tafiyar da shi idan akwai. Bikin takutaha ya qunshi dukkan abubuwan da ake gabatarwa a wannan rana, kama daga karatuttuka da nuna murna ta hanyar nishadi da kuma ziyarce-ziyarcen ‘yan’uwa da abokan arziki.
Karanta: Kun san menene ma’anar Takutaha?
Karatun Takutaha
A ranar takutaha haqiqa ana gabatar da karatuttuka daban-daban. Tun da sassafe malamai kan taru a cikin masallacin Madabo domin gabatar da wannan karatu. Daga cikin karatuttukan da ake gabatarwa akwai waqoqin yabon Annabi salallahu alaihi wasallam. Yawancin wannan waqoqi ana gabatar da su ne da harshen Larabci. Waqar da aka fi karantawa ita ce, Ishiriniya, sannan akwai kari na musamman wanda sai xan Madabo ne ya iya shi. Haka kuma, a cikin baitukan ishiriniyar, kowane gida a Madabo suna da baitinsu wanda suka zava suka nuna sha’awarsu a kai. Don haka, a duk lokacin da aka zo wannan baiti, akan yi wa shugaban wannan gidan addu’a don tunawa da shi (Hira da M.A.M,11-12-2008).
A duk lokacin da ake gabatar da karatun takutaha, ana ganin abubuwan ta’ajibi, domin akwai wani baiti na ishiriniya wanda da zarar an zo wurin, kowa yana miqewa tsaye, domin malamai sun ce, Manzon Allah salallahu alaihi wasallam yana halartar wurin. A wannan lokaci kuma, takardun ishiriniyar da ke hannun masu karatun, sukan tashi sama suna yawo a kan mutane. Haka kuma, makaru da ke jingine a masallacin kan rabu da qasa su zan yi sama (Hassan, 1998:95).
Bayan karatun ishiriniya, ana gabatar da wasu waqoqin yabon Annabi salallahu alaihi wasallam cikin Larabci kamar haka:
Qasidar isma’uli
Isma’uni aqul ya jami’i, ahlul aqul
Wa madahu hazar Rasul haira min yamdahu Muhammad
Marhaba shahru atana wulida fiha Nabina”
Fassarar Hausa
“ku saurare ni zan ambata ya jama’a ma’abota ambato
Yabon wannan Annabi shi ne fiyayyen yabo na Annabi Muhammadu
Marhaba da watan da ya zo mana A cikinsa ne aka haifi Annabinmu”.
Qasidar Muqamul lada
Muqamul lada sudratul muntaha Li Ahmadu la shakka fi Mustapha
Muqamun wa tallahi ma misluhu Fa wahyun Ilaihi shadidil quwa
Lam kallamal Lahu Musa ala Hamdan la shakka lil Mustapha
Wa’inna Nabiyyin Abil Qasimu Habibur risalati fauqas sama
Fassarar Hausa
Muqami mafifici wato sudratul muntaha Ga Ahmadu babu shakka tare da Al-Mustapha
Wallahi babu wani muqami ya wannan wahayi ne daga Allah mai cikakken mulki.
Annabi Musa ya yi magana da Allah godiya, babu shakka ga Al-Mustapha
Haqiqa Annabi baban Alqasim Masoyin saqo daga Allah.
Qasidar Ahlan bi shahril Maulidi
“Ahlan bi shahrul Maulidi Shahrul Nabiy Muhammadi
Huwa bi sa’adil as’adi Khairil Wara Muhammadi”
Fassarar Hausa
Marhaba da watan Maulidi Watan Annabinmu Muhammadu
Shi ne Mafificin masu xaukaka Mafi alhairin Al’umma Annabi Muhammadu”.
Sannan akwai sauran qasidu da dama kamar su: Qasidar iza raka’a zamanu da Rafa’atul Umuri da Asiru zunubi da Xanxarani da Shahrul rabi’i da sauransu.
Rubutu masu alaka:
Duk wanda ya tsere maka a kaunar manzo (s.a.w) ya tsere maka da komai –Limamin Jumu’a
Al’umma na cigaba da raya daren Mauludi a Kano
Marubuci: Tijjani Shehu Almajir
+234(0)8035943092
Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya,
Jami’ar Bayero, Kano.
Addini
Iyaye ku kula da tarbiyyar ƴaƴan ku – Malama Fatima Tsakuwa
Malamar addinin musulunci dake nan Kano Malama Fatima Ahmad Tsakuwa, ta shawarci mata da su ƙara himma wajen kula da tarbiyyar ƴaƴansu, tare da kuma zaburar da su mahimmancin yin addu’a a cikin wannan wata na Ramadana, domin rabauta da rahamar Ubangiji S.W.T.
Malama Fatima Ahmad Tsakuwa, ta bayyana hakan ne yayin taron bita ta musamman da gidauniyar Bango Charity Foundation ƙarƙashin Malama Fatima Yusif Mai tama, wanda gidauniyar ta shirya wa Mata, da bitar ta shafi watan Azumin Ramadana, akan yadda iyaye matan za su kula da ƴaƴan su, da ya gudana a ofishin ƙungiyar dake unguwar Sharaɗa a Kano.
Wakiliyar tashar Dala FM Kano, ta rawaito cewa malama Fatima Tsakuwa ta ce akwai buƙatar iyayen su ƙara lura da tarbiyyar ƴaƴansu, tare da yawaita karatun Al-kur’ani mai girma domin rabauta da falala a wajen Allah S.W.T.
Addini
Ku gujewa saɓawa Ubangiji S.W.T, a cikin watan Azumin Ramadan – Mal. Abubakar na Madabo
Fitaccen malamin addinin musuluncin nan Sheikh Abubakar Kabiru Ibrahim, babban malami na Madabo, ya ja hankalin al’ummar Musulmi, da su kame daga saɓawa Ubangiji S.W.T, yayin watan Azumin Ramadan, domin gujewa fushin sa.
Sheikh Abubakar babban malami na Madabo, ya bayyana hakan ne yayin bikin saukar karatun Al-kur’ani mai girma, na makarantar Huzaifatu Yamani Littahafizul Qur’an Wattarbiyya Al-Islamiyya, ta gudanar karo na uku, na ɗalibai 103, yayin da suka kasance Maza 36, Mata 67, da ta gudanar cikin unguwar Ƙofar Ruwa dake ƙaramar hukumar Dala, a ranar Asabar.
Malamin ya kuma ce akwai buƙatar al’ummar Musulmi, su dage da yawaita karatun Al-kur’ani mai girma, tare da komawa ga Ubangiji S.W.T, tare da salatin Ma’aiki S.A.W, inda ya kuma yi kira ga ƴan kasuwa da su sauƙaƙa wa al’umma domin samun sauƙi daga cikin halin matsin rayuwar da suka samu kansu a ciki.
Da yake nasa jawabin shugaban makarantun na Huzaifatu Yamani a jihar Kano Mallam Anas Muhammad Madabo, ya ce kasancewar makarantun Islamiyya ba su da gata a wajen wasu mutane, sai dai a wajen Ubangiji S.W.T, akwai buƙatar masu hali su shigo wajen tallafawa domin samun damar shayar da ɗalibai ingantaccen Ilmi.
“Iyaye yadda ku ke nuna halin ko in kula da karatun ƴaƴan ku musamman wajen rashin turo su makaranta a kan lokaci, da ƙarancin biyan kuɗin makaranta sai kun dage domin ta haka ne zaku rinƙa ƙara mana ƙwarin gwiwa wajen koyar da ƴaƴan naku, “in ji Mal. Anas Madabo”.
Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa, a nasa ɓangaren shugaban makarantar da ɗaliban suka yi saukar a ƙofar ruwa Mallam Abdullahi Sa’ed Umar, shawartar ɗalibai ya yi da su ƙara himma wajen neman Ilmin addinin da na zamani, domin zama ababen koyi a tsakanin al’umma.
Addini
Zuwan Ramadan: Ku tallafawa mabuƙata bisa halin matsin rayuwar da ake ciki – Dr. Abdallah Gadan Ƙaya
Limamin masallacin Juma’a na Usman Bin Affan dake unguwar Gadan Kaya Dakta Abdallah Usman Umar, ya shawarci al’umma da su ƙara ɗaɓɓaƙa taimakon masu ƙaramin ƙarfi a cikin watan Ramadana dake tafe, domin rabauta da lada a wajen All…S.W.T.
Dakta Abdallah Gadan Kaya, ya bayyana hakan ne ta cikin shirin Rayuwa Abar Koyi da ya gudana a tashar Dala FM, a ranar Juma’a.
Ya ce kasancewar watan Ramadana wata ne mai ɗumbin falala, akwai buƙatar masu hali su tallafawa mabuƙata domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa.
“Mutane ku kasance masu yawaita karatun Al-kur’ani mai girma, da sauran litattafai, domin rabauta da rahamar Ubangiji S W.T, “in ji Dr. Abdallah”.
Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa Dakta Abdallah Gadan Ƙaya, ya ƙara da cewa, akwai buƙatar ƴan kasuwa su sauƙaƙawa al’umma bisa halin matsin rayuwar da aka samu kai yanzu a ciki domin samun sauƙi.
-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai3 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Manyan Labarai4 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Nishadi4 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai4 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya2 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai4 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi4 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su