Connect with us

Addini

Abinda yasa ake hawa dutsen Dala rana Takutaha

Published

on

Hakika hawa dutsen Dala a ranar da ake gabatar da bikin takutaha yana nuna alamun bikin Maguzawa da suke yi a Kano duk shekara, wanda suke hawa dutsen Dala da Gwauron Dutse da Magwan da Fanisau suna gabatar da bukukuwan bauta.

Ganin cewa shi kansa bikin takutaha, malaman Madabo sun qirqire shi ne domin kawar da hankalin matasa da mata daga wadannan bukukuwa na Maguzawa, to da alamun shi ya sa har yanzu a duk ranar bikin takutaha samari da mata da yara suke yin dandazo wajen hawa wannan dutse na Dala.

Duk da cewar su Maguzawa suna gabatar da bautarsu ne bisa jagorancin shugabansu, wato Barbushe wanda yake shiga xakin Tsumburbura ya jiyo musu abin da zai faru a wannan shekarar, kuma ya fito ya sanar da su.

Hoto daga Dutsen Dala a bikin Takutaha na bana

A yanzu ba haka ba ne, domin kuwa sai bayan an gama karatun Madabo kuma babban malami ya yi addu’a an watse. A sannan ne yara da samari suke tafiya domin hawa dutsen Dala. Don haka, ba sharaxin bikin ba ne sai an hau wannan dutsen.

A kan Dala, ana gabatar da abubuwa ne da suka shafi nishaxantarwa da kuma kallon qwaryar birnin Kano. Wasu har hotuna suke xauka. Daga baya, an samu cewar wasu ma suna hawa ne domin su yi shaye-shayen kayan maye da yin caca da kuma faxace-faxacen  ‘yan daba wanda har ta kan kai da ji wa kai rauni. Wannan ba ya rasa nasaba da nason irin yadda maguzawan da suke yin bikinsu a kan dutsen Dalan suke yin shaye-shayen giya da sauransu. Don haka, ana iya kallon wannan gurvacewa a matsayin yadda bikin maguzawan na asali yake a gurvace.

Hoto daga Dutsen Dala a bikin Takutaha na bana

Matsayin Bikin Takutaha

Bikin takutaha muhimmiyar rana ce a cikin garin Kano, domin a wannan rana akan yanke duk wasu hulxoxi a mayar da hankali wajen gudanar da wannan biki, musamman a wajen qananan yara. Dangane da wannan biki kuwa, waxansu suna ganin ba zai rasa alaqa da bautar gunkin Tsumburbura ba, wanda jama’ar Kano suke yi tun kafin zuwan addinin Musulunci (Ibrahim,1982:290). Bukukuwan da Maguzawa suke yi a kan dutsen Dala yana matuqar jan hankalin mata da yara da baqi, don haka sai malaman Madabo suka haxu a masallacin Madabo suka shawarta kan yadda za su xauke hankalin masu zuwa kallon waxannan bukukuwa na Maguzawa.

Manya-manyan malaman wannan zamani da suka zartar da wannan shawara, sun haxa da: Shehu Isa Mai Lawali da Shehu Mamuda mai Mudawwana da Shehu Ibrahim Liman Mai batta da Shehu Sulaiman mai rubutu da sauransu. Haka kuma, an sami wakilcin malamai daga unguwannin Dukurawa da Sheshe da Mandawari da Jujin-‘yanlabu da Maxatai da sauransu (Hassan,1998:97).

Hoto daga Dutsen Dala a bikin Takutaha na bana

Matsayin bikin Takutaha bai wuce ganin an kawar da hankalin yara da mata daga aqidar Maguzanci zuwa tarbiyyar musulunci ba. Wannan shi ne dalilin da ya sa Madabo suka kafa yin Mauludi a wannan unguwa, wanda daga baya ne mutane suka sauya masa suna zuwa Takutaha.

Dangane da sauran al’umma kuwa, wannan rana tana da matsayi sosai a wajensu. A wannan rana sukan sami damar ziyartar dangi waxanda aka daxe ba a haxu ba. Baya ga haka, qananan yara sukan sami walwala da nishaxi a wannan rana, musamman a kan Dala, inda ake kaxe-kaxe da raye-raye. Har wa yau, masu kayan sayarwa suna samun ciniki sosai, kasancewar jama’a suna zuwa daga vangarori daban-daban. Bugu da qari, al’umma suna haxuwa don yi wa kawunansu da garinsu addu’o’i baki daya.

Rubutu masu alaka:

Fitattun hotuna daga bikin Takutaha na bana

Yadda ake gudanar da bikin Takutaha a Kano

Kun san menene ma’anar  Takutaha?

Marubuci: Tijjani Shehu Almajir

almajir02@yahoo.com

+234(0)8035943092

Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya,

Jami’ar Bayero, Kano.

Addini

Iyaye ku kula da tarbiyyar ƴaƴan ku – Malama Fatima Tsakuwa

Published

on

Malamar addinin musulunci dake nan Kano Malama Fatima Ahmad Tsakuwa, ta shawarci mata da su ƙara himma wajen kula da tarbiyyar ƴaƴansu, tare da kuma zaburar da su mahimmancin yin addu’a a cikin wannan wata na Ramadana, domin rabauta da rahamar Ubangiji S.W.T.

Malama Fatima Ahmad Tsakuwa, ta bayyana hakan ne yayin taron bita ta musamman da gidauniyar Bango Charity Foundation ƙarƙashin Malama Fatima Yusif Mai tama, wanda gidauniyar ta shirya wa Mata, da bitar ta shafi watan Azumin Ramadana, akan yadda iyaye matan za su kula da ƴaƴan su, da ya gudana a ofishin ƙungiyar dake unguwar Sharaɗa a Kano.

Wakiliyar tashar Dala FM Kano, ta rawaito cewa malama Fatima Tsakuwa ta ce akwai buƙatar iyayen su ƙara lura da tarbiyyar ƴaƴansu, tare da yawaita karatun Al-kur’ani mai girma domin rabauta da falala a wajen Allah S.W.T.

Continue Reading

Addini

Ku gujewa saɓawa Ubangiji S.W.T, a cikin watan Azumin Ramadan – Mal. Abubakar na Madabo

Published

on

Fitaccen malamin addinin musuluncin nan Sheikh Abubakar Kabiru Ibrahim, babban malami na Madabo, ya ja hankalin al’ummar Musulmi, da su kame daga saɓawa Ubangiji S.W.T, yayin watan Azumin Ramadan, domin gujewa fushin sa.

Sheikh Abubakar babban malami na Madabo, ya bayyana hakan ne yayin bikin saukar karatun Al-kur’ani mai girma, na makarantar Huzaifatu Yamani Littahafizul Qur’an Wattarbiyya Al-Islamiyya, ta gudanar karo na uku, na ɗalibai 103, yayin da suka kasance Maza 36, Mata 67, da ta gudanar cikin unguwar Ƙofar Ruwa dake ƙaramar hukumar Dala, a ranar Asabar.

Malamin ya kuma ce akwai buƙatar al’ummar Musulmi, su dage da yawaita karatun Al-kur’ani mai girma, tare da komawa ga Ubangiji S.W.T, tare da salatin Ma’aiki S.A.W, inda ya kuma yi kira ga ƴan kasuwa da su sauƙaƙa wa al’umma domin samun sauƙi daga cikin halin matsin rayuwar da suka samu kansu a ciki.

Da yake nasa jawabin shugaban makarantun na Huzaifatu Yamani a jihar Kano Mallam Anas Muhammad Madabo, ya ce kasancewar makarantun Islamiyya ba su da gata a wajen wasu mutane, sai dai a wajen Ubangiji S.W.T, akwai buƙatar masu hali su shigo wajen tallafawa domin samun damar shayar da ɗalibai ingantaccen Ilmi.

“Iyaye yadda ku ke nuna halin ko in kula da karatun ƴaƴan ku musamman wajen rashin turo su makaranta a kan lokaci, da ƙarancin biyan kuɗin makaranta sai kun dage domin ta haka ne zaku rinƙa ƙara mana ƙwarin gwiwa wajen koyar da ƴaƴan naku, “in ji Mal. Anas Madabo”.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa, a nasa ɓangaren shugaban makarantar da ɗaliban suka yi saukar a ƙofar ruwa Mallam Abdullahi Sa’ed Umar, shawartar ɗalibai ya yi da su ƙara himma wajen neman Ilmin addinin da na zamani, domin zama ababen koyi a tsakanin al’umma.

Continue Reading

Addini

Zuwan Ramadan: Ku tallafawa mabuƙata bisa halin matsin rayuwar da ake ciki – Dr. Abdallah Gadan Ƙaya

Published

on

Limamin masallacin Juma’a na Usman Bin Affan dake unguwar Gadan Kaya Dakta Abdallah Usman Umar, ya shawarci al’umma da su ƙara ɗaɓɓaƙa taimakon masu ƙaramin ƙarfi a cikin watan Ramadana dake tafe, domin rabauta da lada a wajen All…S.W.T.

Dakta Abdallah Gadan Kaya, ya bayyana hakan ne ta cikin shirin Rayuwa Abar Koyi da ya gudana a tashar Dala FM, a ranar Juma’a.

Ya ce kasancewar watan Ramadana wata ne mai ɗumbin falala, akwai buƙatar masu hali su tallafawa mabuƙata domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa.

“Mutane ku kasance masu yawaita karatun Al-kur’ani mai girma, da sauran litattafai, domin rabauta da rahamar Ubangiji S W.T, “in ji Dr. Abdallah”.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa Dakta Abdallah Gadan Ƙaya, ya ƙara da cewa, akwai buƙatar ƴan kasuwa su sauƙaƙawa al’umma bisa halin matsin rayuwar da aka samu kai yanzu a ciki domin samun sauƙi.

Continue Reading

Trending