Connect with us

Labarai

Kai tsaye :Ana tsaka da fafatawa tsakanin lauyoyi

Published

on

Tuni kotun daukaka kara dake zamanta a kaduna karkashin alkalai 5 ta zauna domin fara sauraron daukaka karar da Jam iyyar PDP da dan takarar gwamna a karkashin jam’iyyar Abba kabir Yusuf suka shigar.

Inda suke rokon kotun da ta rushe hukuncin da mai Sharia Halima Shamaki tayi, wanda ta ayyana Abdullahi Umar Ganduje a matsayin wanda ya yi nasara a zaben shekarar 2019 sakamakon rashin gamsassun hujoji da masu kara suka gaza gabatarwa kamar yanda kotun ta ayyana.

A zaman kotun da ake yi a daidai wannan lokaci lauyoyin hukumar zabe da suka hadar da J B Dawood da A A Raji da Abdulkarim Maude sunyi suka akan yanda aka shigar da karar.

Barrister Dawood ya bayyanawa kotun cewar suna suka akan dalilan daukaka karar.

Hukumar zaben ta bakin lauyoyinta sunyi suka akan dalilai na 1 da 2 na da da na 3 da 8 da 13 da 14 da 15 da 16 da 17da dalili na 18.

Wasu daga cikin ‘yan jam’iyyar PDP kenan a harabar kotun daukaka kara dake Kaduna

Barrister Dawood ya bukaci kotun tayi nazari akan wadannan dalilai ya kuma roki kotun da ta kori daukaka karar sakamakon rashin ingancin dalilan masu daukaka kara

Yayin da yake maida martani lauyan Jam’iyyar PDP Barrister Adebayo Awomolo ya bayyana cewar dalilan daukaka karar suna da inganci.

Magoya bayan jam’iyyar APC a harabar kotun daukaka kara dake Kaduna

Harma ya karanta kunshin wata takarda mai dauke da sadarori 9 ya kuma karanta wata takardar mai kunshe da sadarori 11 wadanda yake bayyana ingancin dalilansu na daukaka karar.

Sai dai lauyan Ganduje Effiong Effiong shima yayi suka akan dalilan daukaka karar inda ya ayyana cewar masu daukaka kara basu da wani dalili na daukaka kara dan haka kotun ta kori daukaka karar.

Labarai

Shugabanni ku fito da sabbin dabaru domin kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta tsadar rayuwa a ƙasa – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Universal Declaration of Human Rights dake jihar Kano, ta ce akwai buƙatar shugabanni suyi abinda ya dace dan ganin an kawo karshen matsalar tsaro, da kuma ta harkar tsaro dake ci gaba da addabar mutane a sassa ƙasar nan.

Daraktan ƙungiyar Kwamared Umar Sani Galadanci, ne ya bayyana hakan yayin zantwarsa da gidan rediyon Dala FM, a ranar Laraba, ya ce yadda ake ƙara samun ƴan ta’adda suna sace mutane tare da kashe su a sassan ƙasar nan, da kuma halin matsin rayuwar da ake fuskanta akwai buƙatar shugabanni suyi abinda ya kamata dan ganin an kawo ƙarshen matsalolin.

“Yawaitar kai hare-haren da ake samu daga ɓangaren ƴan bindiga a cikin al’ummar gari akan kashe su tare da sace su matuƙar ana son a kawo karshen matsalar, sai an ƙara himma wajen samar da makamai ga jami’an tsaro tare da samar da sabbin dabaru domin kawar da matsalar, “in ji Galadanci”.

Wannan dai na zuwa ne kwanaki kaɗan da sako ɗalibai aƙalla su sama da 285, na makarantar Kuriga dake ƙaramar hukumar Chikun ta jihar Kaduna, da ƴan bindiga suka sace su a baya, baya ga wasu ɗaliban da aka sace a wata makarantar Tsangaya a jihar ta Kaduna, wanda ko a jihar Borno ma aka jiyo yadda aka sace ƴan gudun hijira da dama a baya-bayan nan, inda matsalolin tsaron ke ƙara yin gaba a sassan ƙasar nan.

Continue Reading

Labarai

Gwamnan Kano ya kafa kwamitin duba yadda ake rabon tallafin abincin Azumi

Published

on

Gwamnatin Kano ta kafa kwamitin duba yadda ake ciyarwar azumin watan Ramadan, a kananan hokumomin cikin birnin jihar 8, domin sa ido da duba yadda ake gudanar da aikin dafawa da rabawa al’umma abincin.

Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya kafa kwamitin ne ƙarƙashin kulawar mataimakin gwamnan Kano Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, da wasu ƴan kwamitin.

Hakan na zuwa ne dai bayan da gwamna Abba Kabir, ya ziyarci wasu daga cikin wuraren da ake dafa abincin, inda ya nuna rashin jin daɗin sa kan yadda ya ga aikin ke gudana a karamar hukumar kumbotso.

Bayanin hakan ya fito ne ta cikin wata sanarwar da babban mai taimakawa gwamnan Kano, na musamman akan gidajen rediyo Bashir Aminu Fanshekara, ya aikowa manema labarai, ya ce an bayyana Alhaji Danyaro Yakasai, a matsayin wanda zai jagoranci kwamitin mai mambobi 7.

Fanshekara ya ce kwamitin ya fara zagayawa wasu daga cikin mazaɓu dake karamar hukumar kumbotso, domin duba yadda ake dafawa da kuma raba abincin tallafin ga al’umma, inda suka suka fara da mazaɓar Na’ibawa a ranar Asabar 23 ga watan Maris ɗin shekarar 2024.

Continue Reading

Ilimi

Kaduna:- Daliban Kuriga sun sha ki iskar ‘yanci

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta bayar da rahoton cewa an sako duka ɗaliban makarantar Kuriga da ƴanbindiga suka sace.

 

An sace ɗaliban firamare da na sakandare su kusan 287 a makarantarsu da ke ƙauyen Kuriga a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna fiye da makonni biyu da suka wuce.

 

Sanarwar da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya fitar ta ce an sako duka ɗaliban kuma suna cikin koshin lafiya.

 

Sanarwar ba tayi karin bayani ba game da irin matakan da aka bi wajen sako ɗaliban, sai dai gwamna Uba Sani ya nuna godiya ga shugaba Tinubu da mai bashi shawara kan tsaro da kuma sojojin Najeriya saboda irin rawar da suka taka wajen ganin an sako ɗaliban.

 

“Ba dare babu rana ina tattaunawa da Malam Nuhu Ribadu domin lalubo hanyoyin da za a bi wajen kubutar da daliban, kafin mu samu nasara,” in ji Uba Sani.

 

Galibinsu ɗaliban da aka sace ƴan shekaru biyar ne zuwa 18.

Continue Reading

Trending