Connect with us

Labarai

Kai tsaye :Ana tsaka da fafatawa tsakanin lauyoyi

Published

on

Tuni kotun daukaka kara dake zamanta a kaduna karkashin alkalai 5 ta zauna domin fara sauraron daukaka karar da Jam iyyar PDP da dan takarar gwamna a karkashin jam’iyyar Abba kabir Yusuf suka shigar.

Inda suke rokon kotun da ta rushe hukuncin da mai Sharia Halima Shamaki tayi, wanda ta ayyana Abdullahi Umar Ganduje a matsayin wanda ya yi nasara a zaben shekarar 2019 sakamakon rashin gamsassun hujoji da masu kara suka gaza gabatarwa kamar yanda kotun ta ayyana.

A zaman kotun da ake yi a daidai wannan lokaci lauyoyin hukumar zabe da suka hadar da J B Dawood da A A Raji da Abdulkarim Maude sunyi suka akan yanda aka shigar da karar.

Barrister Dawood ya bayyanawa kotun cewar suna suka akan dalilan daukaka karar.

Hukumar zaben ta bakin lauyoyinta sunyi suka akan dalilai na 1 da 2 na da da na 3 da 8 da 13 da 14 da 15 da 16 da 17da dalili na 18.

Wasu daga cikin ‘yan jam’iyyar PDP kenan a harabar kotun daukaka kara dake Kaduna

Barrister Dawood ya bukaci kotun tayi nazari akan wadannan dalilai ya kuma roki kotun da ta kori daukaka karar sakamakon rashin ingancin dalilan masu daukaka kara

Yayin da yake maida martani lauyan Jam’iyyar PDP Barrister Adebayo Awomolo ya bayyana cewar dalilan daukaka karar suna da inganci.

Magoya bayan jam’iyyar APC a harabar kotun daukaka kara dake Kaduna

Harma ya karanta kunshin wata takarda mai dauke da sadarori 9 ya kuma karanta wata takardar mai kunshe da sadarori 11 wadanda yake bayyana ingancin dalilansu na daukaka karar.

Sai dai lauyan Ganduje Effiong Effiong shima yayi suka akan dalilan daukaka karar inda ya ayyana cewar masu daukaka kara basu da wani dalili na daukaka kara dan haka kotun ta kori daukaka karar.

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending