Connect with us

Labarai

Kai tsaye :Ana tsaka da fafatawa tsakanin lauyoyi

Published

on

Tuni kotun daukaka kara dake zamanta a kaduna karkashin alkalai 5 ta zauna domin fara sauraron daukaka karar da Jam iyyar PDP da dan takarar gwamna a karkashin jam’iyyar Abba kabir Yusuf suka shigar.

Inda suke rokon kotun da ta rushe hukuncin da mai Sharia Halima Shamaki tayi, wanda ta ayyana Abdullahi Umar Ganduje a matsayin wanda ya yi nasara a zaben shekarar 2019 sakamakon rashin gamsassun hujoji da masu kara suka gaza gabatarwa kamar yanda kotun ta ayyana.

A zaman kotun da ake yi a daidai wannan lokaci lauyoyin hukumar zabe da suka hadar da J B Dawood da A A Raji da Abdulkarim Maude sunyi suka akan yanda aka shigar da karar.

Barrister Dawood ya bayyanawa kotun cewar suna suka akan dalilan daukaka karar.

Hukumar zaben ta bakin lauyoyinta sunyi suka akan dalilai na 1 da 2 na da da na 3 da 8 da 13 da 14 da 15 da 16 da 17da dalili na 18.

Wasu daga cikin ‘yan jam’iyyar PDP kenan a harabar kotun daukaka kara dake Kaduna

Barrister Dawood ya bukaci kotun tayi nazari akan wadannan dalilai ya kuma roki kotun da ta kori daukaka karar sakamakon rashin ingancin dalilan masu daukaka kara

Yayin da yake maida martani lauyan Jam’iyyar PDP Barrister Adebayo Awomolo ya bayyana cewar dalilan daukaka karar suna da inganci.

Magoya bayan jam’iyyar APC a harabar kotun daukaka kara dake Kaduna

Harma ya karanta kunshin wata takarda mai dauke da sadarori 9 ya kuma karanta wata takardar mai kunshe da sadarori 11 wadanda yake bayyana ingancin dalilansu na daukaka karar.

Sai dai lauyan Ganduje Effiong Effiong shima yayi suka akan dalilan daukaka karar inda ya ayyana cewar masu daukaka kara basu da wani dalili na daukaka kara dan haka kotun ta kori daukaka karar.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending