Connect with us

Labarai

Kai tsaye: An dage cigaba da sauraron karar Abba da Ganduje

Published

on

Kotun daukaka kara dake zamanta a kaduna karkashin alkalai 5 ta kammala sauraron Dalilan daukaka karar Jam iyyar PDP da dan takarar gwamnan Kano a karkashin jam iyyar Abba kabir yusuf wadanda suke kalubalantar nasarar da kotun karbar korafe korafen zaben kano ta bawa Abdullahi umar Ganduje na Jam iyyar APC

A zaman kotun na yau lauyoyin hukumar zabe da karkashin J B Dawood SAN sun roki kotun da ta kori daukaka karar sakamakon kura-kurai da suka ce an yi a yayin shigar.

Lauyan Jam iyyar APC Barrister Effiong Effiong ya bayyana cewar basu da suka akan rokon da hukumar zaben tayi harma yace shi bai ga wata gamsasshiyr hujja da zata sanya a daukaka kara a hukuncin da mai shari’a Halima shamaki tayi wanda ta kori karar da PDP ta shigar bisa rashin gamsassun hujjoji ba.

Sai dai lauyan Jam iyyar PDP Adebayo Owomolo ya bayyana  cewar dalilansu na daukaka kara sahihai ne harma ya karanta wata takarda mai kunshe da sadara 9 ya kuma karanta wata takardar mai kunshe da sadara 11 wanda yake bayyana cewar suna da hujjojin daukaka kara

Har ila yau, Barrister Owomolo ya kuma roki kotun da ta rushe hukuncin Justice shamaki an kuma dage zaman dan yin hukunci.

Wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya zanta da lauyan Abba Barrister Bashir Muhd Tudun-wuzirci

Shima lauyan Ganduje barrister Ma’aruf Muhammad Yakasai ya yi martani

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending