Manyan Labarai
Zaman da majalisar dokokin Kano ta yi a yau laraba.
Majalisar dokokin jihar Kano ta ce za ta yi iya bakin kokarinta wajen tabbatar da gyaran dokar kafa hukumar bunkasawa da Kuma samar da tallafi ga bangaren ilimi ta jihar Kano ta shekarar dubu biyu da goma sha Tara Wanda gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya aike mata.
Mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar Kano Honarabul Hamisu Ibrahim Chidari ne ya bayyana haka yayin karanta wasikar da gwamnan Kano ya turowa majalisar game da gyaran kudirin dokar hukumar mai taken Kano state education development establishment support bill 2019.
Ya ce matukar aka amince da gyare-gyaren da aka yi ga hukumar aka Kuma amince da shi akan lokaci zai bai wa jihar Kano daman fara cin gajiyar tallafi kan harkokin ilimi daga kungiyoyin ba da tallafi kan harkar ilimi a duniya.
Wakiliyar mu ta majalisar dokokin jihar Kano Khadija Ishaq muhammad ta rawaito cewa, majalisar ta bukaci sanya batun gyaran dokar cikin ayyukan da za ta gudanar a zamanta na gaba.
A bangare guda kuma hukumomin gwamnati na cigaba da bayyana gaban kwamatocin zauren majalisar domin kare kasafin kudin su.
Inda Ma’aikatar kananan hukumomin ta jihar Kano ta gabatar da naira biliyan dari biyu da goma sha shida da miliyan sittin da biyu da dubu dari tara da saba’in da uku da dari daya da talatin da shida da Kwabo arbain da hudu a matsayin kunshin kasafin kudin kananan hukumomin jihar arbain da hudu.
Hakan ya biyo bayan karanta wata wasikar da ma’aikatar kananan hukumomi ta aikewa majalisar mai dauke da sa hannun kwamishinan ta Murtala Sule Garo wanda mataimakin shugaban majalisar Hamisu Ibrahim Chidari ya karanta da safiyar yau laraba.
Ta cikin wasikar ta bayyana cewar ma’aikatar kananan hukumomi tayi la’akari da bukatun al’umma, gabanin amincewa da kididdigar kudaden da ta ke muradin kashewa.
Daga nan ne majalisar ta baiwa kwamitocin ta mai kula da kasafin kudi da na kananan hukumomi wa’adin makwanni hudu suyi nazarin kunshin kasafin kafin su dawo da shi gabanta.
Manyan Labarai
Gundura da ake zargi da sarewa Ɗan Bijilante hannu da fasa motar ƴan sanda ya shiga hannu
Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta samu nasarar cafke wani Matashi mai suna Inuwa Zakari ɗan shekara 24, wanda akafi sani da Gundura, wanda ake zargi da sarewa wani Ɗan Bijilante hannu, da kuma fasa motar Ƴan Sanda, da wasu Laifuka
Kakakin rundunar ƴan sandan SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwar da ya aikowa Dala FM a daren Litinin, Kiyawa ya ce Matashi Gundura sun daɗe suna neman sa ruwa a jallo bisa zargin sa da tarin Laifuka.
“Gundura ya kasance abokin fitaccen ɗan Dabar nan Abba Burakita ɗa unguwar Ɗorayi da ya rasu a baya, kuma har kotu ma muka gurfanar da shi daga baya ya fita amma bai dai na abinda ya ke yi ba, a ranar zaɓen ƙananan hukumomin Kano, da ya shigo yana yunƙurin tayar da hankalin al’umma jami’an mu suka kama shi, “in ji SP Kiyawa”.
Har ila yau, Abdullahi ya ce an kama Gundura da wukake guda biyu a wani waje na matattarar Yan Daba da suke kira “Jungle” a Unguwar Dorayi.
Rundunar ƴan sandan ta ce ta kuma cafke ƙarin wasu matasa 14, da ake zargin su da aikata maban-banta laifuka, inda aka kama su a tsakanin 25 ga zuwa 27 na watan Oktoban 2024.
SP Kiyawa ya ƙara da cewa yanzu haka waɗanda ake zargin ana ci gaba da bincike a kan su a babban sashin binciken manyan laifuka na CID, da ke hedikwatar rundunar da ke Bompai a Kano, kuma da zarar an kammala za’a gurfanar da su a gaban kotu.
Manyan Labarai
Ku zauna lafiya yayin zaɓen ƙananan hukumomin da ake gudanarwa a Kano – Kwankwaso
Tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi kira ga al’umma da su tabbatar da an samu zaman lafiya da kwanciyar hankali a zaɓen ƙananan hukumomin da ake gudanarwa yau a Kano.
Sanata Kwankwaso ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kaɗa ƙuri’a a mazaɓar sa ta Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi a Kano.
Ya kuma ce akwai buƙatar al’ummar jihar su fita rumfunan zaɓen su kaɗa ƙuri’un su domin ƙara inganta Demukuraɗiyya a jihar Kano da ma ƙasa baki ɗaya.
Kwankwaso ya kuma jaddada wa al’ummar jihar cewar gwamnatin Kano za ta ci gaba da ayyukan alheri a faɗin jihar, domin samar da ci gaban Jama’a.
A ranar Asabar ɗin nan ne dai ake gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin jihar Kano 44, wanda shugabannin fa za’a zaɓa za su shafe tsawon shekaru uku-uku a karagar mulki.
Kafin wannan rana an dai samu cece-kuce akan batun zaɓen, wanda a ranar Talatar da ta gabata wata babbar kotun tarayya da ke jihar Kano, ta dakatar da shugabancin hukumar zaɓen ta jihar Kanseic, da umartar Ƴan sandan jihar su ƙairacewa shiga aikin zaɓen.
Ko da dai a jiya Juma’a babbar kotun jahar Kano ƙarƙashin mai Shari’a Sunusi Ado Ma’aji, ta umarci hukumar zaɓen ta gudanar da zaɓen a yau Asabar, tare da umartar Ƴan sandan su shiga aikin zaɓen, ko da dai wasu mazauna jihar sun shaidawa Dala FM cewar, ba su ga jami’an ƴan sanda ba a wuraren zaɓen.
Jami’an tsaron da aka gani sun haɗar da ƴan Karota, da na Hisbah, da kuma ƴan Bijilante, da jami’an rundunar tsaro da ke yaƙi da ƙwacen Waya da faɗan Daba da magance Shaye-shaye ta Anty Snaching Phone da ke Kano.
Manyan Labarai
Har yanzu jam’iyyu 6 ne suka cika ƙa’idar zaɓen ƙananan hukumomin da za a gudanar kuma babu APC a ciki – KANSEIC
Hukumar zaɓe ta jihar Kano (KANSIEC), ta bayyana sunayen jam’iyyu 6 a matsayin waɗanda suka cika ƙa’idar shiga zaben ƙananan hukumomin da za a gudanar ranar Asabar a Kano.
Shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan Malumfashi ne ya bayyana hakan jim kaɗan bayan babbar kotun jaha ta tabbatar da halaccin hukumar zaben.
Farfesa Malumfashi ya bayyana cewar jam’iyyun da suka cika ƙa’idar sun haɗar da Jam’iyyar AA, AAC, Accord, ADC, da APM da kuma jam’iyyar NNPP mai mulki a jihar Kano.
Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, shugaban hukumar zaben ya bukaci hukumomin tsaro da su fito su kare rayuka da dukiyoyin al’umma a lokacin gudanar da zaben, kamar yadda babbar kotun jaha ta umarce su a hukuncin da ta yi da ranar Juma’a 25 ga watan Oktoban 2024.
A ranar Alhamis dai an jiyo yadda kwamoshina mai kula da harkokin yaɗa labarai da al’amuran Shari’a na hukumar zaɓe ta jihar Kano Kanseic, Lawan Badamasi, ya ce za su yi amfani da jami’an tsaron cikin gida domin samar da tsaro yayin zaɓen.
Ya ci gaba da cewa daga cikin jami’an tsaron cikin gidan akwai irin su ƴan Karota, da na Hisbah, da kuma Ƴan Bijilante, domin samar da tsaro idan ƴan sanda suka ƙauracewa shiga aikin zaɓen kamar yadda suka samu umarnin hakan daga wata babbar kotun tarayya da ke jihar Kano.
-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya2 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su