Connect with us

Manyan Labarai

Zaman da majalisar dokokin Kano ta yi a yau laraba.

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta ce za ta yi iya bakin kokarinta wajen tabbatar da gyaran dokar kafa hukumar bunkasawa da Kuma samar da tallafi ga bangaren ilimi ta jihar Kano ta shekarar dubu biyu da goma sha Tara Wanda gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya aike mata.

Mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar Kano Honarabul Hamisu Ibrahim Chidari ne ya bayyana haka yayin karanta wasikar da gwamnan Kano ya turowa majalisar game da gyaran kudirin dokar hukumar mai taken Kano state education development establishment support bill 2019.

Ya ce matukar aka amince da gyare-gyaren da aka yi ga hukumar aka Kuma amince da shi akan lokaci zai bai wa jihar Kano daman fara cin gajiyar tallafi kan harkokin ilimi daga kungiyoyin ba da tallafi kan harkar ilimi a duniya.

Wakiliyar mu ta majalisar dokokin jihar Kano Khadija Ishaq muhammad ta rawaito cewa, majalisar ta bukaci sanya batun gyaran dokar cikin ayyukan da za ta gudanar a zamanta na gaba.

A bangare guda kuma hukumomin gwamnati na cigaba da bayyana gaban kwamatocin zauren majalisar domin kare kasafin kudin su.

Inda Ma’aikatar kananan hukumomin ta jihar Kano ta gabatar da naira biliyan dari biyu da goma sha shida da miliyan sittin da biyu da dubu dari tara da saba’in da uku da dari daya da talatin da shida da Kwabo arbain da hudu a matsayin kunshin kasafin kudin kananan hukumomin jihar arbain da hudu.

Hakan ya biyo bayan karanta wata wasikar da ma’aikatar kananan hukumomi ta aikewa majalisar mai dauke da sa hannun kwamishinan ta Murtala Sule Garo wanda mataimakin shugaban majalisar Hamisu Ibrahim Chidari ya karanta da safiyar yau laraba.

Ta cikin wasikar ta bayyana cewar ma’aikatar kananan hukumomi tayi la’akari da bukatun al’umma, gabanin amincewa da kididdigar kudaden da ta ke muradin kashewa.

Daga nan ne majalisar ta baiwa kwamitocin ta mai kula da kasafin kudi da na kananan hukumomi wa’adin makwanni hudu suyi nazarin kunshin kasafin kafin su dawo da shi gabanta.

Manyan Labarai

Bamu da wata alaƙa akan dakatar da Ganduje daga jam’iyyar APC – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya ce basu da wata alaƙa da rikicin cikin gidan da ya kunno kai akan dakatar da Ganduje daga cikin jam’iyyar APC, a Kano.

Babban daraktan yaɗa labaran gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM a yau Laraba.

Ya ce zargin da jam’iyyar APCn Kano ta yi a kan gwamnatin Kano, kan cewar tana da hannu akan dakatar da shugaban ta na riƙo a matakin ƙasa Abdullahi Umar Ganduje, zargin bashi da tushe ballantana makama.

A baya-bayan nan ne dai wani sashi na shugabancin jam’iyyar APC, a mazaɓar Ganduje da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa, ya bayyana dakatar da Abdullahi Ganduje daga cikin jam’iyyar.

Sai dai daga bisani shugaban jam’iyyar na ƙaramar hukumar ya musanta batun dakatarwar inda ya ce ana shirin ɗaukar matakin da ya dace akan wanda ya fitar da sanarwar.

Bature, ya kuma ce lamarin rikici ne na cikin gidan jam’iyyar ta APC, wanda ya kamata su tsaya su gyara, mai-makon mayar da hankali akan gwamnatin Kano, lamarin da ba za suyi nasara ba.

“Tsagin jam’iyyar APCn, Kano suje can kada su ƙara tsomo mu a cikin rikicin su domin bamu da alaƙa da wani rikicin su ko wani abu, “in ji Sunusi”.

Ya kuma ce ko da yaushe jam’iyyar NNPP, mai mulki a jihar Kano burin su shine ci gaba da taimakawa al’ummar jihar ta hanyar damar da ayyukan ci gaban su.

Dawakin Tofa, ya kuma ƙara da cewa Ganduje bashi da tasiri ko da a ƙaramar hukumar sa ballantana kuma azo batun jahar Kano.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Manyan Labarai

Jam’iyyar NNPP ta dakatar da Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf

Published

on

Tsagin jam’iyyar NNPP ta ƙasa karkashin jagorancin Major Agbo, ya sanar da dakatar da Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf daga cikin jam’iyyar.

A cikin wata sanarwa da sakataren jam’iyyar ta ƙasa Ogini Olaposi, ya fitar a yayin taron ‘yan jarida a Talatar nan a Abuja, tsagin jam’iyyar ta NNPP, ya ce rashin bayyana a gaban kwamitin ladabtarwar jam’iyyar da Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi shine ya sanya su ɗaukar wannan mataki.

Ya ƙara da cewa matakin na zuwa ne sakamakon fusata da jam’iyyar ta yi kan halartar wani babban taron jam’iyyar da gwamnan ya yi wanda tsagin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya jagoranta a ranar 6 ga watan Afrilun nan na shekarar 2024. kamar yadda jaridar THE PUNCH ta rawaito.

Sai dai tuni wasu ƴan Kwankwasiyyar suka yi watsi da wannan dakatarwa.

Dambarwar dai na zuwa ne yayin da itama jam’iyyar APC, ke ci gaba da fuskantar ta ta dambarwar, musamman ma da aka jiyo yadda wani sashi na shugabancin jam’iyyar a mazaɓar Ganduje a ƙaramar hukumar Dawakin Tofa, aka jiyo shi ya dakatar da shugaban riƙo na APC ta ƙasa Abdullahi Umar Ganduje, daga cikin jam’iyyar.

Sai dai daga bisani shugabancin jam’iyyar ta APC, a ƙaramar hukumar Dawakin Tofa, ya musanta batun dakatarwar lamarin da yace ma ana shirye-shiryen ɗaukar mataki akan waɗanda suka bayyana dakatarwar.

Continue Reading

Trending