Connect with us

Labarai

Gwamnati za ta dauki mataki kan duk wanda ta samu da cin zarafin dan jarida

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce za ta dauki mataki kan duk wanda ta samu da cin zarafin dan Jarida, duba da muhimmancin aikin na manema labarai a fannin cigaba, Isar da sako da kuma bayar da gudunmawa wajen tsaro a fadin jihar Kano da kasa baki daya.

Kwamishinan ma’aikatar yada labarai na Jihar Kano malam Muhammad Garba, ya bayana haka lokacin da tawagar shugabanin tashoshin Freedom Radio Kano, Jigawa da Kaduna da kuma Dala Fm Kano suka ziyarce shi, karkashin jagorancin manajan daraktan tashoshin Malam Abbas Dalhatu.

Yayin ziyarar taya murna ga Kwamishinan yada labaran, Ya ce akwai kyakkyawar alaka tsakanin gwamnatin Kano da manema labarai.

Dan haka gwamnati za tayi duk abinda ya kamata wajen ciyar da jihar dama ‘yan jarida gaba.

A nasa jawabin manajan maraktan tashoshin Freedom da Dala Fm Kano, Malam Abbas Dalhatu, ya ce makasudin ziyarar shi ne taya kwamishinan murna tare da bayar da shawara kan yadda za a samu nasarar aikin da aka sa gaba dan bunkasa jihar Kano.

Wakilinmu Abba Isah Muhammad, ya ruwaito kwamishinan na cewa kofa abude take don yin aiki tare da kafafen yada labarai matukar abinda zai kawo cigaban jihar Kano ne ko kasa baki daya.

 

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending