Connect with us

Labarai

Wasu kauyuka a Kano sun fara amfani da bahaya a matsayin taki

Published

on

Mutanen garin kududdufawa dake y ankin karamar hukumar Ungogo sun fara sarrafa bahayar mutane suna yin taki dan sayarwa ga manoma suna samun abinda za su ciyar da iyalansu.

Wakilin mu Yusuf Nadabo ya ziyarci dajin malale dake kauyen kududdufawa a karamar hukumar Ungogo inda ya iske bahaya tsubi tsubi danye da busasshe da kuma wanda aka nike shi aka dura a buhunhuna.

Ya kuma iske wasu mutane malam Idi da Isa Musa wadanda sune suke sarrafa bahayar harma Isa Musa ke bayyana cewar suna busar da turoson ta hanyar bada masa wani sinadari.

Domin ya daina doyi kuma ya bushe cikin kankanin lokaci daga nan su fitar da duk wani datti dake jikin turoson su kuma nike shi su dura a buhu daga nan ya zama kudi.

Isa Musa ya bayyana cewar suna sayar da buhun nikakken bahaya a naira dari da hamsin kuma suna samun bahayar ne daga masu kwaso shi daga gidajen mutane.

A duk rana ana samun motocin yar kurkura kamar sawu 20 kuma kowace kurkura tana dakko duro 4 idan aka kawo sais u sarrafa shi su sayar da shi.

Ya kuma bayyana cewar baya nadamar yin sana’ar tunda dai ba kayan wani ya sata ba.

Ya kuma bayyana cewar yana da mata da yaya harda marayu da yake rike da su.

Shima wani mai aikin turoson mai suna malam Idi ya bayyana cewar ba sa kallon sana’ar ta su da kaskanci tunda tana biya musu bukatu.

Sai dai wasu na kallon yin taki da turoso na da illa ga amfanin gona da al’umma.

Ko menene illar yin tasarrafi da turoso ga lafiyar mutane da amfanin gona ku bibiyi shirin rahotanni daga yan zazu na gobe Alhamis dan ji daga bakin masana.

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending