Addini
Kai tsaye: Ma’anar bikin Maukibi da akeyi yau a Kano

Ku cigaba da bibiyar wannan shafi domin ana cigaba da sabinta shi.
Maukibi dai biki ne da mabiya darikar kadiriyya ke gabatarwa duk shekara a birnin Kano.
A yayin bikin dai mabiya darikar kadiriyya na yin jerin gwano daga shalkawatar darikar kadiriyyan ta Africa wato gidan shugaban darikar na Afrcia marigayi Sheikh Nasiru Kabara zuwa masallacin jumu’a na Jami’u Kanzil Mudalsami dake kan titin Katsina a birnin Kano.

Hoto yayin gudanar da maukibi a Kano
A wannan masallacin ne ake gudanar da addu’o’I da kuma jawabai daga jagororin taron a kowacce shekara.

Hoto yayin gudanar da maukibi a Kano
A duk shekara dai bikin Maukibi yana fara kankama ne daga ranar Laraba inda ake gudanar da bukukuwa, karatuka, da addu’o’I a gidan Kadiriyya dake unguwar Kabara a nan Kano.
Daga bisani kuma ranar Asabar a fita zuwa bikin na maukibi wanda ake yiwa lakabi da bikin waliyai.

Hoto yayin gudanar da maukibi a Kano
Al’umma daga kasashe daban-daban na duniya, da kuma wasu jihohin Najeriya da birane da kuma kauyuka na shigowa jihar Kano domin halartar bikin Maukibin.

Hoto yayin gudanar da maukibi a Kano
A yau Asabar 12 ga watan Disamba na shekara ta 2019 ake gabatar da bikin Maukibin na bana, wanda shi ne karo na 69.
Yayin wata tattaunawa da Dala FM tayi da shugaban darikar kadiriyya na Africa a daren jiya Sheikh Dakta Kariballahi Nasiru Kabara ya bayyana cewa babban sakonsa a wannan taron shi ne kira ga al’umma kan a zauna lafiya domin tabbatar da hadin kai da cigaba ga al’ummar mu.

Hoto yayin gudanar da maukibi a Kano
Kai tsaye dai muna kawo muku yadda bikin yake gudana ta akwatunan rediyonku akan mita 88.5 a zangon FM.
Labarai masu alaka:
Al’umma na cigaba da raya daren Mauludi a Kano
Yadda ake gudanar da bikin Takutaha a Kano

Addini
Hukumar Shari’a ta shirya buɗe baki ga Mutanen da suka musulunta a Kano

A ƙoƙarin ta na ƙara ɗaɓɓaƙa harkokin addinin Musulunci, hukumar Shari’ah ta jihar Kano da haɗin guiwar kungiyar World Assembly of Muslim Youth (Wamy), sun shirya wa waɗanda suka karbi addinin Musulunci shan ruwa a ranar Lahadi 23 ga Ramadan shekarar 1446.
Taron shan ruwan dai ya gudana ne a harabar hukumar karkashin Jagorancin Mukaddashin Shugaban ta Sheikh Ali Ɗan Abba.
Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Muƙaddashin Daraktan yaɗa labarai na hukumar shari’a ta jihar Kano, Musa A Ibrahim (Best Seller).
Hukumar Shari’ar ta kuma ayyana ranar 15 ga Ramadan domin ta zama ranar da za ta rinƙa shan ruwa da waɗanda suka karɓi addinin Musulunci da za a rinƙa yi a duk shekara.
“Muna kuma miƙa godiya ga gwamnatin jihar Kano a karkashin gwamna Abba Kabir Yusuf, da ƙungiyar World Assembly of Muslim Youth [WAMY] da suka ba mu gudummawa wajen shirya wannan taron, “in ji Sheikh Ali”.
Taron shan ruwan dai ya sami halartar dukkanin shugabannin hukumar da mambobin ta da kuma ma’aikatanta tare da shugabannin kungiyar WAMY, da wasu manyan mutane da suka halarta.
Da yake nasa jawabin wakilin shugaban kungiyar Wamy Alhaji Sanusi, ya nuna jin daɗinsa da yadda wannan shan ruwa ya gudana, kuma ya tabbatar da cewar kungiyar su ƙungiya ce ta taimakon addinin musulunci da musulmi a ko ina suke, kuma kungiyar zata ci gaba da wannan aikin alherin da izinin Allah S.W.T.

Addini
Ku taimakawa mabuƙata da Naman Sallah bisa halin matsin rayuwar da ake ciki – Limami

Babban limamin masallacin juma’a na Alaramma Abubakar Ɗan Tsakuwa, da ke unguwar Ja’en Ring road Mallam Abdulkareem Aliyu, ya yi kira ga al’ummar Musulmi, da su kiyaye ƙa’idojin yanka Dabbobin Layyah, domin gujewa cin mushen Nama.
Mallam Abdulkareem Aliyu, ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u, lokacin da yake tsokacin huɗubar da ya gabatar ranar Sallar Idin da ya jagoranta a masallacin ranar Lahadi 17 ga watan Yunin 2024.
Ya ce a mafi yawan lokuta al’umma sukan yanka dabbobi amma rashin bin ƙa’idojin yanka yakan sanya wa su ci mushen nama ba tare da sun sani ba, a dan haka su tashi tsaye wajen sanin yadda ake yanka Dabbobin a mahanga ta addinin Musulunci.
A cewar sa, “Musulmai ku kwaɗaitu da yin sadakar naman layya musamman ma ga masu ƙaramin ƙarfi domin rabauta da rahamar Ubangiji S.W.T, “in ji shi”.
Mallam Abdulkareem Aliyu, ya kuma ce, akwai buƙatar a kiyaye nau’ikan dabbobin da aka sahale ayi layya da su, waɗanda suka haɗar da nau’in Sa ko Saniya, da kuma Raƙumi ko Raƙuma (Taguwar), ko kuma Rago ko Tinkiya, ko Akuya ko kuma Ɗan Akuya.
Wannan dai na zuwa ne bayan da al’ummar Musulmin Duniya suka gudanar da babbar Sallah, a jiya Lahadi 16 ga watan Yunin shekarar 2024.

Addini
An ga jinjirin watan Zul-Hijjah a Najeriya, ranar Lahadi 16 ga watan Yuni Babbar Sallah

Fadar mai alfarma sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Abubakar Sa’ad na uku, ta sanar da ganin jinjirin watan Zul-Hijjah na shekarar 1445.
Hakan na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da fadar Sarkin Musulmin ta fitar, mai ɗauke da sa hannun Wazirin Sakkwato, kuma shugaban kwamitin duban wata Farfesa Sambo Wali Junaid.
Sanarwar ta kuma ce duba da ganin jaririn watan na Zul-Hijjah da akayi a jiya Alhamis, hakan ya tabbatar da cewar yau Juma’a ɗaya ga watan Zul-Hijjah, wanda za’ayi babbar Sallah a ranar Lahadi 16 ga watan Yunin 2024.
Tun dai a jiya Alhamis hukumomi a ƙasar Saudiyya suka sanar da ganin Jaririn watan na Zul-Hijjah, lamarin da ya kasance za’ayi tsayuwar Arafa a ranar Asabar 15 ga watan Yunin 2024, yayin da za’ayi babbar Sallah a ranar Lahadi 16 ga watan na Yuni.
Kafar Dala FM Kano, ta rawaito cewa, kawo yanzu dai maniyyata aikin hajjin bana da dama ne ke ci gaba da shiga ƙasa mai tsarki, a ƙoƙarin su na zuwa domin sauke Farali.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su