Connect with us

Labarai

Matasa sunyi aure ba tare da sanin iyayensu ba a Kano

Published

on

An gurfanar da wasu matasa biyu da aka boye sunayensu mazauna yankin Kurna dake nan Kano, a gaban hukumar Hisbah ta jiha kan sunyi aure ba tare da sanin iyayensu ba.

Tunda farko dai matasan ne suka hangi yadda wasu mata da miji suke soyayya a yayinda suke wucewa ta gabansu, hakan yasa suka ga baza su iya jurewa ba, don haka suka nemi abokanansu kan suyi musu walicci wajen daura musu aure.

Hakan kuwa akayi inda a karshe abokanansu suka zama waliyan ango dana amarya aka kuma daura auren akan sadaki naira dubu ashirin, ango ya bada naira dubu biyu amarya kuma ta ranta masa naira dubu goma sha takwas.

Tsawon wata uku kenan da aka daura wannan aure, inda Ango da Amarya suke cigaba da mu’amalarsu a matsayin saurayi da budurwa, sai dai wani abin mamaki shi ne wannan aure har ya kai ga yanzu haka an samu rabo, domin kuwa amaryar tuni ta samu juna biyu.

Wakilinmu Ibrahim Abdullahi Soron Dinki ya nemi zantawa da ango da amarya amma danginsu suka ki amincewa.

Mataimakin babban Kwamandan hukumar Hisbah Malam Shehu Tasi’u Ishaq ya ce auren bai dauru ba tunda mahaifin yarinya yana nan a raye, amma ‘dan dake cikin amaryar idan an haifeshi ba za’a kirashi da ‘dan gaba da fatiha ba, suma kuma ba za’a kirasu da sunyi zina ba.

Kazalika Shehu Tasi’u yaja hankalin ma’auratan da suke fitowa fili suna soyayya, yace su sani kunya jigoce ta imani rashinta kuwa jigone na karancin imani, saboda haka yake jan kunne ga ma’aurata dasu rika kiyayewa, saboda rashin hakan kan jawo tabarbarewar tarbiyyar al’umma.

Idan zaku iya tunawa dai a watan Yulin da ya gabata ne akayi wata dambarwa kan wasu matasa da suka daura auren wasa a dandalin sada zumunta na Facebook wanda Hisbah da hukumomin shari’a a Kano suka sha alwashin daukar mataki akai.

Labarai masu alaka:

Baba Suda: Hisbah ta hana cakuduwar maza da mata a cikin babur mai kafa uku

Hisbah ta yiwa wasu ‘yan “Good Evening” ritaya

Labarai

Zamu yi aiki kafaɗa da kafaɗa da ƴan Jarida – Hukumar Zaɓe ta Kano

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSEC, ta sha alwashin aiki kafaɗa-kafaɗa da ma’aikatan Jarida, musamman ma da zaɓen ƙananan hukumomin jihar nan 44 da ke tafe.

Sabon shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan Manumfashi, ne ya bayyana hakan, yayin ziyarar da tawagar ƙuniyar matasan ƴan Jarida, ta Kano Youth Journalist Forum, suka kai masa a ofishin sa yau Alhamis, yayin da ya shafe kwanaki huɗu da kama aiki.

Ya kuma ce, za su yi aiki da ma’aikatan Jarida musamman ma yayin gudanar da ayyukan zaɓen ƙananan hukumomin Kano 44, da ke tafe, domin wayar da kan al’umma da ma samun nasara yayin zaɓen da ma bayan sa.

Farfesa Manumfashi, ya kuma ƙar da cewa, akwai buƙatar kowa ya bayar da tasa gudummawar a harkar zaɓe, domin kuwa yanzu haka suna ci gaba da aiki wajen shirya zaɓen ƙananan hukumomin.

Da yake nasa jawabin shugaban ƙungiyar matasa ƴan Jaridar ta jihar Kano Musa Zangina Adam, ya ce sun kai ziyarar ne, domin su ƙulla alaƙar aiki a tsakanin su da hukumar, bisa yadda kowanne ɓangare yake buƙatar juna, tare kuma da bayar da gudunmawar da ya kamata.

Zangina, ya kuma ce a shirye ƙungiyar su take wajen ci gaba da bibiyar al’amuran da suka shafi al’umma, tare da nusar da mahukunta dan ganin an wadata su da kayayyakin more rayuwa.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Trending