Connect with us

Addini

Bada taimakon Naira 10 a masallatai zai rage talauci ga musulamai- Malam Murtala

Published

on

Hukumar shari’a musulunci ta jihar Kano, ta ce da al’ummar musulmai za su rinka bada taimakon naira 10 a kowane masallacin juma’a da tuni ba a sami yaran da suke tallace-tallace a kan titi da kuma mutanen da suke neman kudin taimako na rashin lafiya a jihar Kano.

Daraktan yada addinin musulunci na hukumar, Muratala Muhammad Adam ne, ya bayyana hakan yayin taron limaman masallatan juma’a wanda ya gudana a karamar hukumar Dawakin Kudu.

Ya ce akwai bukatar al’umma da su rinka amfani da damar su wajen taimakon juna ta hanyar amfani da masallatai.

Ya kuma ce da za a rinka tattara kudaden da ake bayarwa a masallatai da an rinka tallafawa mata suna karatun aikin likita.

Shi kuwa a nasa jawabin yayin taron shugaban hukumar na karamar hukumar Dawakin Kudu,Abdulkarim Husseini Abdulkarim, cewa al’umma da su yi amfani da damar su yun a yanzu.

wakilin mu Tijjani Adamu, ya rawaito cewa taron limaman ya samu halartar limaman masallatan kananan hukumomin Warawa da na Dawakin Kudu.

 

 

 

 

 

 

Addini

Iyaye ku kula da tarbiyyar ƴaƴan ku – Malama Fatima Tsakuwa

Published

on

Malamar addinin musulunci dake nan Kano Malama Fatima Ahmad Tsakuwa, ta shawarci mata da su ƙara himma wajen kula da tarbiyyar ƴaƴansu, tare da kuma zaburar da su mahimmancin yin addu’a a cikin wannan wata na Ramadana, domin rabauta da rahamar Ubangiji S.W.T.

Malama Fatima Ahmad Tsakuwa, ta bayyana hakan ne yayin taron bita ta musamman da gidauniyar Bango Charity Foundation ƙarƙashin Malama Fatima Yusif Mai tama, wanda gidauniyar ta shirya wa Mata, da bitar ta shafi watan Azumin Ramadana, akan yadda iyaye matan za su kula da ƴaƴan su, da ya gudana a ofishin ƙungiyar dake unguwar Sharaɗa a Kano.

Wakiliyar tashar Dala FM Kano, ta rawaito cewa malama Fatima Tsakuwa ta ce akwai buƙatar iyayen su ƙara lura da tarbiyyar ƴaƴansu, tare da yawaita karatun Al-kur’ani mai girma domin rabauta da falala a wajen Allah S.W.T.

Continue Reading

Addini

Ku gujewa saɓawa Ubangiji S.W.T, a cikin watan Azumin Ramadan – Mal. Abubakar na Madabo

Published

on

Fitaccen malamin addinin musuluncin nan Sheikh Abubakar Kabiru Ibrahim, babban malami na Madabo, ya ja hankalin al’ummar Musulmi, da su kame daga saɓawa Ubangiji S.W.T, yayin watan Azumin Ramadan, domin gujewa fushin sa.

Sheikh Abubakar babban malami na Madabo, ya bayyana hakan ne yayin bikin saukar karatun Al-kur’ani mai girma, na makarantar Huzaifatu Yamani Littahafizul Qur’an Wattarbiyya Al-Islamiyya, ta gudanar karo na uku, na ɗalibai 103, yayin da suka kasance Maza 36, Mata 67, da ta gudanar cikin unguwar Ƙofar Ruwa dake ƙaramar hukumar Dala, a ranar Asabar.

Malamin ya kuma ce akwai buƙatar al’ummar Musulmi, su dage da yawaita karatun Al-kur’ani mai girma, tare da komawa ga Ubangiji S.W.T, tare da salatin Ma’aiki S.A.W, inda ya kuma yi kira ga ƴan kasuwa da su sauƙaƙa wa al’umma domin samun sauƙi daga cikin halin matsin rayuwar da suka samu kansu a ciki.

Da yake nasa jawabin shugaban makarantun na Huzaifatu Yamani a jihar Kano Mallam Anas Muhammad Madabo, ya ce kasancewar makarantun Islamiyya ba su da gata a wajen wasu mutane, sai dai a wajen Ubangiji S.W.T, akwai buƙatar masu hali su shigo wajen tallafawa domin samun damar shayar da ɗalibai ingantaccen Ilmi.

“Iyaye yadda ku ke nuna halin ko in kula da karatun ƴaƴan ku musamman wajen rashin turo su makaranta a kan lokaci, da ƙarancin biyan kuɗin makaranta sai kun dage domin ta haka ne zaku rinƙa ƙara mana ƙwarin gwiwa wajen koyar da ƴaƴan naku, “in ji Mal. Anas Madabo”.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa, a nasa ɓangaren shugaban makarantar da ɗaliban suka yi saukar a ƙofar ruwa Mallam Abdullahi Sa’ed Umar, shawartar ɗalibai ya yi da su ƙara himma wajen neman Ilmin addinin da na zamani, domin zama ababen koyi a tsakanin al’umma.

Continue Reading

Addini

Zuwan Ramadan: Ku tallafawa mabuƙata bisa halin matsin rayuwar da ake ciki – Dr. Abdallah Gadan Ƙaya

Published

on

Limamin masallacin Juma’a na Usman Bin Affan dake unguwar Gadan Kaya Dakta Abdallah Usman Umar, ya shawarci al’umma da su ƙara ɗaɓɓaƙa taimakon masu ƙaramin ƙarfi a cikin watan Ramadana dake tafe, domin rabauta da lada a wajen All…S.W.T.

Dakta Abdallah Gadan Kaya, ya bayyana hakan ne ta cikin shirin Rayuwa Abar Koyi da ya gudana a tashar Dala FM, a ranar Juma’a.

Ya ce kasancewar watan Ramadana wata ne mai ɗumbin falala, akwai buƙatar masu hali su tallafawa mabuƙata domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa.

“Mutane ku kasance masu yawaita karatun Al-kur’ani mai girma, da sauran litattafai, domin rabauta da rahamar Ubangiji S W.T, “in ji Dr. Abdallah”.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa Dakta Abdallah Gadan Ƙaya, ya ƙara da cewa, akwai buƙatar ƴan kasuwa su sauƙaƙawa al’umma bisa halin matsin rayuwar da aka samu kai yanzu a ciki domin samun sauƙi.

Continue Reading

Trending