Connect with us

Labarai

Tura dalibai makaranta akan lokaci zai taimaka masu–Mallam Shehu Ali

Published

on

Wani Malamin Addinin musulunci a jihar Kano, Mallam Shehu Ali Abdullahi, ya gargadi iyaye dasu rinka tura ya’yansu makarantu akan lokaci domin kara inganta karatunsu sakamakon daliban na zuwa makaranta a kurarran lokaci.

Mallam Shehu Ali Abdullahi, ya bayyana hakan ne a yayin saukar karatun Alkur’ani mai girma na makarantar Tahir Islamiyya dake unguwar Dorayi karama a yankin karamar hukumar Kumbotso dake jihar Kano wanda ya wakana a karshen makon da ya gabata.

Ya na mai cewa “Iyaye su rinka tura ya’yan su makarantu akan lokaci wanda hakan zai kara sanya yaran za su samu karatu da tarbiyya mai dorewa, kuma hakan zai magance makara da dalibai ke yi wajen tafiya makaranta da wuri”. Inji Malamin.

Da yake nasa jawabin shugaban makarantar, Mallam Muhammad Mustapha Adamu, cewa ya yi” Makarantar tana fuskantar tarin matsaloli musamman ma matsalar abun zama da kuma biyan kudin makaranta daga wurin iyaye wanda har idan iyaye suna bada kudin makaranta akan lokaci da tuni mun magance wasu daga cikin matsalolin mu”.

wasu daga cikin daliban da suka yi saukar Karatun Alkur’anin mai girma sun bayyana farin cikin harma suka tabbatar da cewa zasu yi aiki da abun da suka amfana.

Wakilin mu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa, dalibai maza da mata 74 ne suka yi saukar, yayin da al’umma da dama suka samu damar halartar daga ciki kuwa akwai dagacin Garin Dorayi, Alhaji Umar Shehu Sani.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending