Connect with us

Labarai

Masarautar Ringim ta yi kira a karfafa zumunci

Published

on

Boran Dan Ruwatan Ringim, Alhaji Muhammad Aminu Isah, ya nemi al’ummar musulmai da su kara himmatuwa wajen sada zumunci domin rabauta da rahamar Allah (S.W.T)

Alhaji Muhammad Aminu Isah, ya yi wannan kiran ne a yayin da iyalan Mallam Alhassan Lasan, suka shirya taron sada zumunci, wanda ya gudana a unguwar Sani mai Nagge dake yankin karamar hukumar Gwale a Kano.

Ya ce “Sada zumuncin a tsakanin juna abu ne da yakan kara karfafa zumunta a cikin al’umma baki daya kuma hakan yakan kara dankon zumunci ga ‘yan uwa da abokan arziki”.

Shi kuwa Shugaban hada taron, Mallam Abubakar Sabo Isah, ya ce”Suna hada taron ne domin karfafa  zumunci a tsakanin su musamman ma ta yadda dangin su za s uke shaida ‘yan uwan su a duk inda suke a fadin duniya”.

Hakazalika itama a nata jawabin shugaba a bangaren mata, Hajiya Saude Zakariyya, ta ce” Iyaye da su rinka gudanar da auren zumunci a tsakanin dangi domin hakan zai karfafa zumunci a tsakanin juna da kuma bunkasa zuri’a sakamkon a zamanin yanzu ba’a fiye samun damar yin hakan ba”.

Wakilin mu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa, ‘yan uwa daga cikin ahalin Mallam Alhassan Lasan ne suka halarci taron sada zumuncin wadanda suka zo daga jihohi daban daban daga fadin cikin kasar Nijeriya.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending