Connect with us

Labarai

NDLEA : ta yi wawan kamu a Kano

Published

on

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA reshen jihar Kano, ta kama wata babbar motar daukar kaya da tabar wiwi da nauyinta yakai fiye da kilogiram Dari Takwas, da ake basaja ana safarar tabar wiwi zuwa Jahohin Kaduna, Kano da jigawa.

Kwamandan hukumar a nan Kano Dr Ibrahim Abdul a zantawarsa da manema labarai da yammacin yau Laraba, Ya bayyana cewa sun kame motar ne da mutane hudu a daren jiya talata a Garin Kwanar Dan Gora, lokacin da wadanda ake zargin suke sauke tabar wiwin da karfe Uku da rabi na dare.

Ibrahim Abdul, Ya kara da cewar cikin wadanda suka kama akwai maza Uku da mace daya, kuma yace da zarar sun kammala bincike zasu gurfanar dasu a gaban kotu.

Suma wadanda ake zargin sun bayyana yadda suka shiga hannu tare da bayana ladamar su.

Wakilmu Abba Isah Muhammad, Ya ruwaito mana cewar Mai tuka motar ya tsere sai dai hukumar ta NDLEA ta kama yaran motar mai suna Aliyu Baban Gida,da wani mai suna Hamza Abubakar Dan Batta da Sani Bala wanda yace yana safarar tabar Wiwin Zuwa Jigawa da nan Kano, ya kuma ce wannan zai zamu na karshe, sai kuma macen mai suna Sumayya Abubakar, wadda tace bata da masaniyar mijinta yana Saida tabar Wiwin.

 

 

 

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending