Connect with us

Manyan Labarai

An kama dalibin jami’a a Kano da shigar mata

Published

on

Dalibin wanda ya ke aji na biyu  wato Level Two a jami’ar Wudil dake jiahr Kano an kama shi ne  a ranar Talatar nan sanye da kayan matan lokacin da ya labe a cikin bandakin mata bayan an yi masa ihu ne aka kamashi aka mikawa mahukuntar makarantar.

A zantawar gidan rediyon Dala da wasu daliban jami’ar mata sun tabbatar da cewa an kama shi harma an dakatar da shi yanzu haka wanda ake zargin da aikata hakan.

Sun kuma ce” A bandakin mata muka ji ihu nan take muka sanar da jani’an tsaron makarantar a ka kuma kama shi. Bayan an kama shi sai a ka kuma tambaye shi a ina ya samu kayan matan ciki harda nikafi sai ya ce dama suna wurin sa, kuma ko da aka tambaye shi mai yazo yi bangaren mata sai ya ce ya shigo ne domin ya kalli mata ya kuma yi sata”. A cewar wasu daga cikin daliban da muka zanta dasu.

Yanzu haka dai dalibin har an lika hoton sa tare da kayan mata da sunan sa da lambar sa ta karatu ciki harma aka bayyana cewa kwamatin ladabtarwa ya dakatar da shi ahr sai sun zauna a kan batun.

Mun kuma yi kokarin jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na makarantar Sa’idu Abdullahi Nayaya ta wayar tarho ya ce a saurare su za su bada nasu bayanin amma har zuwa wannan lokaci na kamala rahotan basu bada nasu jawabin ba.

Manyan Labarai

APC ta dakatar da Dakta Abdullahi Ganduje daga jam’iyyar

Published

on

Jam’iyyar APC ta dakatar da tsohon gwamnan jihar Kano kuma shugaban jam’iyyar na kasa Dakta Abdullahi Umar Ganduje daga jam’iyyar.

Mai bai wa jam’iyyar shawara a ɓangaren shari’a a mazaɓar Ganduje, da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa, Halliru Gwanzo, ya bayyana hakan ne a zantawar sa da manema labarai a jihar ta Kano, kamar yadda jaridar online ta Nigerian Triker ta rawaito.

Halliru Gwanzo, ya kuma ce sun ɗauki matakin dakatar da tsohon gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ne sakamakon zarge-zargen da gwamnatin jihar Kano take masa a kan yin badaƙala da kuɗin al’ummar jahar.

Continue Reading

Manyan Labarai

Gwamnan Kano ya yi alƙawarin gyara titin garin Kundila da ke ƙaramar hukumar Shanono

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta yi alkawari gyara titin da ya taso daga babban titin karamar hukumar Shanono zuwa garin Kundila da ke karamar hukumar.

Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusif, ne ya bayyana hakan yayin ta’aziyyar da ya kai na rasuwar ɗan majalisar dokokin jiha mai wakiltar ƙananan hukumomin Ɓagwai da Shanono Honorable Halilu Ibrahim Kundila.

Marigayin dai ya rasu ne a makon da ya gabata.

Gwamna Abba Kabir Yusif ya kuma bayyana kaɗuwar sa a lokacin da yaji rasuwar Marigayin, inda ya ce mutum ne mai gaskiya da rukon amana.

Wakilinmu na fadar gwamnatin jihar Kano Abba Haruna Idris ya rawaito cewa, Abba Kabir ya kuma ce gwamnatin Jihar Kano za ta dauki nauyin karatun iyalan mamacin daga inda suka tsaya har su kammala karatun nasu.

Continue Reading

Manyan Labarai

Fitacciyar Jarumar Kannywood Saratu Giɗaɗo (Daso) ta rasu

Published

on

Fitacciyar Jaruma a masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood Saratu Gidaɗo wadda akafi sani da Daso, ta rasu a yau Talata.

Mijin ƙanwar marigayiya Daso, kuma mai baiwa gwamnan Kano shawara a kan harkokin tafiye-tafiye da shaƙatawa Mustapha Ibrahim Chidari, ne ya tabbatar wa wakilinmu Bashir Sharfaɗi rasuwar ta a ranar Talata.

Ya ce da Asubar yau tayi Sahur, ta koma Bacci, sai dai kuma zuwa wajen ƙarfe 10 na safe aka ga bata fito daga ɗakin ta ba, ko da aka shiga ɗakin ne aka tarar ta rasu.

Mustapha, ya ce za’a yi jana’izar ta da yammacin Talatar nan, da misalin ƙarfe 04:30 a gidanta dake Chiranchi cikin garin Kano.

Marigayiya Daso, guda ce daga cikin fitattun jarumai a masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, wadda ta shafe shekaru a masana’antar.

Continue Reading

Trending