Connect with us

Manyan Labarai

Hukumar Hisba ta tarwatsa gidan wata kawaliya.

Published

on

Hukumar Hisba ta jihar Kano ta yi nasarar tarwatsa gidan wata mata da ake zargin ta na kawalcin maza da mata a unguwar Danbare, inda aka yi zargin wasu ‘yan matan na tarewa a gidan suna aikata Badala.

Daga cikin wadanda ake zargin sun tare a gidan har da wata matashiya Hadiza wacce ta bar gidan iyayenta su ke ta neman ta.

Daga bisani dai iyayen nata su ka je hukumar ta Hisba domin ta nemo ma ta ‘yar ta su, inda hukumar ta baza jami’anta suna bin gidajen da ake zarginsu da aikata badala, bincikensu kuma ya gano cewar ta na gidan matar da ake zarginta da yin kawalci, su ka kamo ta da sauran wasu matan har dama ita matar da ake zargin, kuma da zuwan su hukumar aka fara yi musu gwajin cutar HIV.

Wakilinmu Ibrahim Abdullahi Soron Dinki ya zanta da wani daga cikin ‘yan’uwan samarin da aka kama a gidan inda ya ce, “Wannan ita ce take jan su, saboda kamar yadda aka fada wannan tsohuwa kowa ya na ganinta za ta je ta samu yaran (may be) kila cikin iya magana, kuma wannan yaro sana’arsa ma kafinta ya na taimakawa iyayensa, musamman ma mahaifiyarsa, idan aka je aka gaya ma ta za ta ce ba halinsa ba ne.

Matasan da aka kama a gidan sun nuna nadamar su, kuma su ka ce wannan shi ne karo na karshe ba za su kuma aikatawa ba.

Sai dai wacce ake zargin, ta ce ba za ta yi magana a rediyo ba, inda ta kuma bada hanzarinta da cewar, ita ba kawaliya ba ce kasuwanci ta ke a wannan gida.

Mataimakin Babban Kwamandan hisbar kan al’amuran yau da kullum wanda Malam Tasi’u Ishak ya ce, “Babu shakka duk inda kaga tsohon banza to asali yaron banza ne, saboda haka idan aka samu irin wannan, matakin da za’a dauka shi ne mataki na hukuma, ta yadda za a kai ga alkali, shi kuma alkali ya yi hukuncin da ya dace.”

Ya kuma kara da cewar, “Duk sanda namiji ko mace ya dauki harkar fasikanci sana’a, to ya na kan fadawa cikin garari, saboda haka tabbacin akwai cutar ko babu sai (result) sakamako ya fito, daga nan ne mutum zai san babu, kuma ko mutum yaga babu bai hana anjima ya kamu da cutar ba idan ya ci gaba da yi.”

Wakilin namu ya so jin ta bakin ‘yan matan suma amma sai su ka ki cewa komai.

Manyan Labarai

Bamu da wata alaƙa akan dakatar da Ganduje daga jam’iyyar APC – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya ce basu da wata alaƙa da rikicin cikin gidan da ya kunno kai akan dakatar da Ganduje daga cikin jam’iyyar APC, a Kano.

Babban daraktan yaɗa labaran gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM a yau Laraba.

Ya ce zargin da jam’iyyar APCn Kano ta yi a kan gwamnatin Kano, kan cewar tana da hannu akan dakatar da shugaban ta na riƙo a matakin ƙasa Abdullahi Umar Ganduje, zargin bashi da tushe ballantana makama.

A baya-bayan nan ne dai wani sashi na shugabancin jam’iyyar APC, a mazaɓar Ganduje da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa, ya bayyana dakatar da Abdullahi Ganduje daga cikin jam’iyyar.

Sai dai daga bisani shugaban jam’iyyar na ƙaramar hukumar ya musanta batun dakatarwar inda ya ce ana shirin ɗaukar matakin da ya dace akan wanda ya fitar da sanarwar.

Bature, ya kuma ce lamarin rikici ne na cikin gidan jam’iyyar ta APC, wanda ya kamata su tsaya su gyara, mai-makon mayar da hankali akan gwamnatin Kano, lamarin da ba za suyi nasara ba.

“Tsagin jam’iyyar APCn, Kano suje can kada su ƙara tsomo mu a cikin rikicin su domin bamu da alaƙa da wani rikicin su ko wani abu, “in ji Sunusi”.

Ya kuma ce ko da yaushe jam’iyyar NNPP, mai mulki a jihar Kano burin su shine ci gaba da taimakawa al’ummar jihar ta hanyar damar da ayyukan ci gaban su.

Dawakin Tofa, ya kuma ƙara da cewa Ganduje bashi da tasiri ko da a ƙaramar hukumar sa ballantana kuma azo batun jahar Kano.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Manyan Labarai

Jam’iyyar NNPP ta dakatar da Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf

Published

on

Tsagin jam’iyyar NNPP ta ƙasa karkashin jagorancin Major Agbo, ya sanar da dakatar da Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf daga cikin jam’iyyar.

A cikin wata sanarwa da sakataren jam’iyyar ta ƙasa Ogini Olaposi, ya fitar a yayin taron ‘yan jarida a Talatar nan a Abuja, tsagin jam’iyyar ta NNPP, ya ce rashin bayyana a gaban kwamitin ladabtarwar jam’iyyar da Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi shine ya sanya su ɗaukar wannan mataki.

Ya ƙara da cewa matakin na zuwa ne sakamakon fusata da jam’iyyar ta yi kan halartar wani babban taron jam’iyyar da gwamnan ya yi wanda tsagin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya jagoranta a ranar 6 ga watan Afrilun nan na shekarar 2024. kamar yadda jaridar THE PUNCH ta rawaito.

Sai dai tuni wasu ƴan Kwankwasiyyar suka yi watsi da wannan dakatarwa.

Dambarwar dai na zuwa ne yayin da itama jam’iyyar APC, ke ci gaba da fuskantar ta ta dambarwar, musamman ma da aka jiyo yadda wani sashi na shugabancin jam’iyyar a mazaɓar Ganduje a ƙaramar hukumar Dawakin Tofa, aka jiyo shi ya dakatar da shugaban riƙo na APC ta ƙasa Abdullahi Umar Ganduje, daga cikin jam’iyyar.

Sai dai daga bisani shugabancin jam’iyyar ta APC, a ƙaramar hukumar Dawakin Tofa, ya musanta batun dakatarwar lamarin da yace ma ana shirye-shiryen ɗaukar mataki akan waɗanda suka bayyana dakatarwar.

Continue Reading

Trending