Connect with us

Labarai

Zamu yiwa masu sha’awar mallakar bindiga lasisi- Rundunar ‘yansanda

Published

on

Rundunar yansandan jihar Katsina karkashin kwamishinan yansandan jihar, CP Sanusi Buba, ta ce ta samu nasarar bindige wasu mutane 2 da sukayi garkuwa da wani mutum mai suna Poul Lawan a karamar hukumar Malumfashi dake jihar Katsina.

Kakakin rundunar, SP Gambo Isa, shi ne ya bayyana hakan yayin ziyarar aiki da wakilin gidan radiyon Dala Yusuf Nadabo Ismail ya kai jihar.

SP Gambo Isa ya ce” Mun yi musayar wuta da wasu mutane a dajin Jigawar Shawai dake karamar hukumar Dan musa mun kuma samu nasarar harbe wani mai suna Gambo Malajo da wani mai suna Ali Dan Mai Shago wadanda suka sace wata yarinya suka nemi kudin fansa har Naira miliyan biyu”.

Kakakin ya kuma ce” Mun kuma kubutar da wata matashiya wadda aka sace aka boye ta a dajin Barawa dake karamar hukumar Batagarawa. A cikin watanni biyu mun kubutar da mutane da dama sun kuma kama yanfashi da barayin shanu”. A cewar SP Gambo.

Wakilin mu ya kuma tambayi SP Gambo dangane da mallakar bindiga ga farar hula, sai ya ce” A shirye muke mu yiwa mutanen da suke kananan hukumomi 8 lasisin mallakar bindiga domin kare kai tunda dokar kasa ta yadda da hakan, kuma za ka iya harbe duk wani bata gari da yake neman cutar da kai musamman ma har idan ya shigo cikin gidan ka, domin ko addinin ya ba ka damar kare kanka. Kuma kiran mu ga matasa da su rinka shiga aikin kato da gora wato na ‘yan sintiri ko kuma aikin ‘yansandan cikin jama’a na PCRC, kuma ku tabbata kuna zuwa wajen turawan ‘yansanda yankunan ku domin koyon dabarun aiki”.Inji SP Gambo.

A karshe muna kira ga duk wani mai garkuwa da mutane ya mika wuya in kuma an ki ji to ba ka ki gani ba, saboda wannan Karin babu zabi wajen sasanci tsakanin mu da ku”. SP Gambo.

 

Labarai

Shugabanni ku fito da sabbin dabaru domin kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta tsadar rayuwa a ƙasa – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Universal Declaration of Human Rights dake jihar Kano, ta ce akwai buƙatar shugabanni suyi abinda ya dace dan ganin an kawo karshen matsalar tsaro, da kuma ta harkar tsaro dake ci gaba da addabar mutane a sassa ƙasar nan.

Daraktan ƙungiyar Kwamared Umar Sani Galadanci, ne ya bayyana hakan yayin zantwarsa da gidan rediyon Dala FM, a ranar Laraba, ya ce yadda ake ƙara samun ƴan ta’adda suna sace mutane tare da kashe su a sassan ƙasar nan, da kuma halin matsin rayuwar da ake fuskanta akwai buƙatar shugabanni suyi abinda ya kamata dan ganin an kawo ƙarshen matsalolin.

“Yawaitar kai hare-haren da ake samu daga ɓangaren ƴan bindiga a cikin al’ummar gari akan kashe su tare da sace su matuƙar ana son a kawo karshen matsalar, sai an ƙara himma wajen samar da makamai ga jami’an tsaro tare da samar da sabbin dabaru domin kawar da matsalar, “in ji Galadanci”.

Wannan dai na zuwa ne kwanaki kaɗan da sako ɗalibai aƙalla su sama da 285, na makarantar Kuriga dake ƙaramar hukumar Chikun ta jihar Kaduna, da ƴan bindiga suka sace su a baya, baya ga wasu ɗaliban da aka sace a wata makarantar Tsangaya a jihar ta Kaduna, wanda ko a jihar Borno ma aka jiyo yadda aka sace ƴan gudun hijira da dama a baya-bayan nan, inda matsalolin tsaron ke ƙara yin gaba a sassan ƙasar nan.

Continue Reading

Labarai

Gwamnan Kano ya kafa kwamitin duba yadda ake rabon tallafin abincin Azumi

Published

on

Gwamnatin Kano ta kafa kwamitin duba yadda ake ciyarwar azumin watan Ramadan, a kananan hokumomin cikin birnin jihar 8, domin sa ido da duba yadda ake gudanar da aikin dafawa da rabawa al’umma abincin.

Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya kafa kwamitin ne ƙarƙashin kulawar mataimakin gwamnan Kano Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, da wasu ƴan kwamitin.

Hakan na zuwa ne dai bayan da gwamna Abba Kabir, ya ziyarci wasu daga cikin wuraren da ake dafa abincin, inda ya nuna rashin jin daɗin sa kan yadda ya ga aikin ke gudana a karamar hukumar kumbotso.

Bayanin hakan ya fito ne ta cikin wata sanarwar da babban mai taimakawa gwamnan Kano, na musamman akan gidajen rediyo Bashir Aminu Fanshekara, ya aikowa manema labarai, ya ce an bayyana Alhaji Danyaro Yakasai, a matsayin wanda zai jagoranci kwamitin mai mambobi 7.

Fanshekara ya ce kwamitin ya fara zagayawa wasu daga cikin mazaɓu dake karamar hukumar kumbotso, domin duba yadda ake dafawa da kuma raba abincin tallafin ga al’umma, inda suka suka fara da mazaɓar Na’ibawa a ranar Asabar 23 ga watan Maris ɗin shekarar 2024.

Continue Reading

Ilimi

Kaduna:- Daliban Kuriga sun sha ki iskar ‘yanci

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta bayar da rahoton cewa an sako duka ɗaliban makarantar Kuriga da ƴanbindiga suka sace.

 

An sace ɗaliban firamare da na sakandare su kusan 287 a makarantarsu da ke ƙauyen Kuriga a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna fiye da makonni biyu da suka wuce.

 

Sanarwar da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya fitar ta ce an sako duka ɗaliban kuma suna cikin koshin lafiya.

 

Sanarwar ba tayi karin bayani ba game da irin matakan da aka bi wajen sako ɗaliban, sai dai gwamna Uba Sani ya nuna godiya ga shugaba Tinubu da mai bashi shawara kan tsaro da kuma sojojin Najeriya saboda irin rawar da suka taka wajen ganin an sako ɗaliban.

 

“Ba dare babu rana ina tattaunawa da Malam Nuhu Ribadu domin lalubo hanyoyin da za a bi wajen kubutar da daliban, kafin mu samu nasara,” in ji Uba Sani.

 

Galibinsu ɗaliban da aka sace ƴan shekaru biyar ne zuwa 18.

Continue Reading

Trending