Manyan Labarai
Ba’amurkiya da masoyin ta sun hada cinkoso a kasuwar Sabon Gari

Masoyan biyu sun dai kai ziyara ne kasuwar Muhammdu Abubakar Rimi dake sabon Gari a jihar Kano a yau Alhamis domin yin siyayyar kayan auren na su.
Ba Amurka Janine Sanchez mai shekaru 46 da haihuwa yar asalin jihar Carlifonia dake can kasar ta Amurk wadda ta yi tsaiwar daka kan cewar sai ta auri Sulaiman Isah Panshekara mai shekaru 23 da haihuwa wanda suka hadu a shafin sada zumunta na instgarm, kuma abun mamakin shi ne duk kokarin da mahukunta da sauran al’umma ke yin a ankarar da shi Sulaiman din kan illar aurar baturiyar ta yi burus da kalubalantar da ake yi mata na biyo sahibin na ta har garin Panshekara dake karamar hukumar Kuimbotso a jihar Kano.
Sai dai kuma a yau dinnan kasuwar ta Sabon Gari ta na tsaka da ciki sai masoyan suka bayyana a kasuwar domin yin siyayyar kayayyakin auren su lamarin da ya dau hankalin yan kasuwar da masu siyayya wanda kallo ya koma kan su lamarin da ya janyo siyayyar ta gagare su saboda yan hoton selfie da masoyan biyu.
Sakamakon cincirindon al’ummar zuwa yanzu ba a iya kayyade iya adadin mutanen da suka nuna bukatar su domin daukar hoto da masoyan ba wanda ya janyo siyayyar kayan auren ta gagara sai kai musu kayan a kayi har ofishin sarkin kasuwar.
Mun kuma zanta da sakataren sarkin kasuwar ta sabon gari, Sulaiman Adamu Indabo wanda ya ce” Mune muka kai su ofishin mu domin yawon mutanen ya kai yawan das ba za a iya iyakance sub a saboda farin jinin masoyan da suke shirin angon cewa”.
Mun kuma yi kokarin jin ta bakin masoyan amma hakar mu bai cimma ruwa ba.

Labarai
Za mu ci gaba da karɓar tsofaffin kuɗi a Singa har nan da kwanaki 2 – Habibu Fantiya

Wani ɗan kasuwa dake kasuwar Singa a jihar Kano ya ce, Alhaji Habibu Yusuf Abdullahi Fantiyahar zuwa nan da kwanaki biyu za su ci gaba da karbar kudade a shagunansu, sai dai idan bankuna sun yi musu barazanar daina karbar tsofaffin kudi za su dakata.
Alhaji Habibu Yusuf Abdullahi Fantiya, ya bayyana hakan ne a zantawarsa da wakilin mu na ‘yan Zazu, Abubakar Sabo, yana mai cewar, al’umma daga garuruwa daban-daban sun shigo kasuwar, idan suka daina karɓar tsofaffin kuɗi za a cutar da su.
Akwai cikakken rahoton a muryar da ke kasa.

Manyan Labarai
Majalisar dattijai ta bukaci CBN ya Kara wa’adin amfani da tsaffin kudi

Mako guda gabanin daina amfanin da tsaffin takardun kudaden naira 200 da 500 da Kuma 1000, majalisar dattawan Kasar nan ta bukaci Babban bankin kasa CBN da ya Kara wa’adin har zuwa 30 ga watan Yuni.
Cikin wani kudiri da sanata Sadik Suleman daga Jihar kwara ya gabatar a zaman majalisar na wannan rana.
Majalisar ta bukaci CBN da ya tsawaita lokacin har zuwa watanni 6 masu zuwa.
Majalisar ta kafa hujja da yanayin tattalin arzikin kasa, da Kuma korafe korafen jama’a, a don haka ta bukaci CBN da ya tsawaita lokacin amfanin da tsaffin kudin har zuwa 30 ga watan Yuni.
Batun sauyin takardun kudin dai na cigaba da samun mabanbantan ra’ayoyi daga ‘yan Nigeria, koda dai a baya bayan cikin wata tattaunawa da akayi da shugaban kasa Muhammadu Buhari, yace ” batun sauyin takardun kudin ba gudu ba ja da baya.

Manyan Labarai
Na sauke nauyin da ‘yan Nigeria suka dora min – Buhari

Shugaba Muhammadu Buhari ya ce ya mulki Najeriya da iyakar ƙokarinsa, inda ya ce bai ba wa ‘yan ƙasar kunya ba.
Shugaban wanda ya je jihar Bauchi a cigaba da ƴaƙin neman zaɓen jam’iyyar APC na shugaban ƙasa da kuma na gwamna, ya bayyana hakane lokacin da ya kai ziyara gidan Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Suleiman Adamu.
Buhari ya ce dubban mutane da suke fitowa su tarbe shi a duk inda ya je hakan na nuna ƙarara irin soyayyar da ake masa.
“Ina so na faɗa cewa tsakanin 2003 zuwa 2011, na kai ziyara dukkanin ƙananan hukumomin Najeriya, sannan a 2019, lokacin da nake neman sake komawa kan mulki ƙaro na biyu, na ziyarci dukkanin jihohi a faɗin ƙasar, mutanen da naga sun fito tarba ta, abu ne da ba zan iya misaltawa ba saboda dandazonsu, a lokacin na yi alkawarin mulkar Najeriya da ‘yan Najeriya da iyaƙar ƙokarina kuma zuwa yanzu na san na yi ƙokari,” in ji shugaban.
Tun da farko a jawabinsa, Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Suleiman, ya ce abu mai kyau ne idan shugabannin siyasa suka nuna girmamawa ga Sarakuna da kuma masarautu ta hanyar kai musu ziyara.
Ya godewa shugaba Buhari kan irin ci gaban da gwamnatinsa ta kawo a Bauchi, inda ya ce aikin haƙo man fetur na Kolmani, wani bu ne da ‘yan jihar da ma arewa maso gabas ba za su manta ba.

-
Nishadi3 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Manyan Labarai3 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai3 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Nishadi3 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai2 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Lafiya8 months ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Nishadi3 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai3 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano