Connect with us

Manyan Labarai

Ba’amurkiya da masoyin ta sun hada cinkoso a kasuwar Sabon Gari

Published

on

Masoyan biyu sun dai kai ziyara ne kasuwar Muhammdu Abubakar Rimi dake sabon Gari a jihar Kano a yau Alhamis domin yin siyayyar kayan auren na su.

Ba Amurka Janine Sanchez mai shekaru 46 da haihuwa yar asalin jihar Carlifonia dake can kasar ta Amurk wadda ta yi tsaiwar daka kan cewar sai ta auri Sulaiman Isah Panshekara mai shekaru 23 da haihuwa wanda suka hadu a shafin sada zumunta na instgarm, kuma abun mamakin shi ne duk kokarin da mahukunta da sauran al’umma ke yin a ankarar da shi Sulaiman din kan illar aurar baturiyar ta yi burus da kalubalantar da ake yi mata na biyo sahibin na ta har garin Panshekara dake karamar hukumar Kuimbotso a jihar Kano.

Sai dai kuma a yau dinnan kasuwar ta Sabon Gari ta na tsaka da ciki sai masoyan suka bayyana a kasuwar domin yin siyayyar kayayyakin auren su lamarin da ya dau hankalin yan kasuwar da masu siyayya wanda kallo ya koma kan su lamarin da ya janyo siyayyar ta gagare su saboda yan hoton selfie da masoyan biyu.

Sakamakon cincirindon al’ummar zuwa yanzu ba a iya kayyade iya adadin mutanen da suka nuna bukatar su domin daukar hoto da masoyan ba wanda ya janyo siyayyar kayan auren ta gagara sai kai musu kayan a kayi har ofishin sarkin kasuwar.

Mun kuma zanta da sakataren sarkin kasuwar ta sabon gari, Sulaiman Adamu Indabo wanda ya ce” Mune muka kai su ofishin mu domin yawon mutanen ya kai yawan das ba za a iya iyakance sub a saboda farin jinin masoyan da suke shirin angon cewa”.

Mun kuma yi kokarin jin ta bakin masoyan amma hakar mu bai cimma ruwa ba.

 

Manyan Labarai

Aƙalla shaguna 180 ne suka ƙone a gobarar babbar kasuwar jihar Sokoto

Published

on

Rahotanni na bayyana cewa wata gobara da ta tashi a babbar kasuwar jihar Sokoto, ta yi sanadiyyar ƙonewar shaguna da dama a ɓangaren masu sayar da babura da kekuna, da safiyar Litinin ɗin nan.

Shugaban ƙungiyar ƴan mashin reshen jihar ta Sokoto, Garba Muhammad Gwazi, ne ya bayyana hakan a zantwarsa da BBC, ya ce gobarar ta laƙume shaguna ‘180’ na masu sayar da babura a cikin kasuwar.

“Sai dai har yanzu ba’a san abin da ya janyo tashin gobarar ba da ta janyo asarar dukiya ta miliyoyin Naira. gobarar ta soma ne daga wata shara da aka tara amma gobarar ba ta kai ga asarar rai ko jikkata kowa ba, “in ji shi”.

Haka kuma Gwazi, ya kuma yi kira ga gwamnati da ta kai musu ɗauki, domin kasuwancin su ya miƙe ya ci gaba da tafiya yadda ya kamata.

A nasa jawabin mai bai wa gwamnan jihar Sokoto shawara kan babbar kasuwar Honarabul Ibrahim Muhammad Giɗaɗo, ya ce wutar ta tashi da sanyin safiyar yau Litinin.

A cewar sa, “Ɓangaren da ya ƙone sosai a cikin kasuwar shi ne na ƴan babura da kekuna, ana iya samun shago guda ɗauke da mashin fiye da 200 ko 100, shagunan gaba ɗaya sun ƙone,”.

Giɗaɗo ya ƙara da cewa jami’an kashe gobara sun kashe kashi 80 cikin 100 na gobarar da ke ci.

Ya ci gaba da cewa, “Waɗannan baburan akwai waɗanda suka haura miliyan, akwai asara mai yawa.”.

Continue Reading

Manyan Labarai

Gwamnan Kano ya gwangwaje ma’aikatan gidan gwamnatin jihar da kayan abinci da kuɗaɗe

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya ce zai ci gaba da gudanar da ayyukan alheri ga ma’aikatan musamman idan suka tsaya tsayin daka a kan ayyukan su na dai-dai.

Injiniya Abba Kabir ya bayyana hakan ne yayin bayar da tallafin kayan abinci na miliyoyin Naira ga ma’aikatan gidan gwamnatin da su ke aiki tare da shi, a wani ɓangare na watan Ramadan mai alfarma.

Bayanin hakan na ƙunshe ne ta cikin wata takarda mai ɗauke da sa hannun babban daraktan yaɗa labaran Gwamnan Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a jiya Lahadi, jim kaɗan da bayar da tallafin kayan abincin.

Daga cikin waɗanda suka ci gajiyar tallafin abincin sun haɗar da ma’aikata daga matakin aiki na 1 zuwa na 12, haka kuma kayan da aka basu sun haɗar da buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 50, da katon macaroni, sai buhun gero mai kwano 10, da kuma kudi N10,000 kowannen su.

Yayin da yake gabatar da kayayyakin cikin yanayi na musamman, gwamnan ya bayyana godiyarsa ga Allah da ya ba shi damar yin hakan da nufin ganin an samu nasara ga ma’aikatan sa a cikin watan Ramadan mai albarka.

A cewar sa, “Yau rana ce ta Musamman a gare ni har ma’aikata na a gidan gwamnati domin na fara cika alkawuran yakin neman zabe da na inganta ayyukan jin dadi ga ma’aikatan gwamnati.” in ji gwamnan”.

Gwamnan Abba Kabir ya ƙara da cewa, dangantakar sa da ma’aikatan ba ta iya siyasa ba ce, a dan haka za su iya yin ra’ayoyin su daban-daban, amma abin da yake buƙata daga gare su shi ne sadaukarwa, aiki tukuru, da addu’a domin su cimma abin da suke yi a fagen aiki.

Daga nan sai ya yi kira gare su da su yi amfani da watan Ramadan ta hanyar yawaita ayyukan ibada tare da yin addu’a ga gwamnati da kasa baki daya Allah ya kawo mana dauki, musamman a wannan lokaci na matsin rayuwa.

Da yake jawabi tun da farko mataimakin gwamnan jihar Kano Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, ya yabawa gwamnan bisa wannan karamcin da ya nuna, inda ya bayyana hakan a matsayin irinsa da aka taba samu a jihar.

Har ila yau, Kwamared Abdussalam ya yi kira ga waɗanda suka ci gajiyar shirin rabon kayan abincin da su mayar da hankali wajen sadaukar da ayyukansu, tare da rikon amana, da addu’a ga gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf, domin ci gaba da samar da ayyukan alheri ga al’ummar jihar.

Continue Reading

Manyan Labarai

Muna Allah wa dai da dakatar da Sanata Abdul Ningi har wata uku – Ƙungiyar matasan ƴan Jarida ta Kano

Published

on

Ƙungiyar matasan ƴan jarida reshen jihar Kano, wato Kano Youth Journalist Forum, ta yi kira ga majalisar dattawan ƙasar nan, da ta gaggauta janye dakatar da Sanata Abdul Ahmed Ningi, da ta yi har tsawon watanni uku a baya-bayan nan, bisa tauye masa haƙƙi da ma na waɗanda yake wakilta a zauren majalisar dattawa.

Shugaban ƙungiyar matasan ƴan jaridar Musa Zangina Adam, ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ƙungiyar ta gudanar, ya ce basa goyon bayan dakatar da Sanata Abdul Ningi, duba da yadda yake ƙokarin kare muradun al’ummar Arewacin ƙasar nan, la’akari da yadda ya rinƙa ƙoƙari akan cushen da ya yi zargin an yi, a cikin kasafin kuɗin 2024.

A makon da ya gabata ne dai majalisar dattawan ta bakin shugaban ta Godswill Akpabio, ta bayyana dakatar da Sanata Abdul Ningi, daga ayyukan majalisar bisa zargin sa da zubar da kimar majalisar, inda a hirar sa da sashen Hausa na BBC, ya zargi majalisar da yin cushe a kasafin kudin ƙasa na 2024, lamarin da bayan amincewar mafi rinjayen ƴan majalisar aka dakatar da Ningi tsawon watanni uku.

“Muna kira da babbar murya ga masu ruwa da taki da su yi duba na tsakani domin ganin an janye dakatar da Sanata Abdul Ningi, ya ci gaba da aikinsa a zauren Majalisar dattawa domin ci gaba da wakiltar al’ummar sa; kuma muna Allah wa dai da dakatar da sanata Ningi, “in ji Zangina”.

Musa Zangina ya kuma ƙara da cewa, La’akari da cewa yanzu al’ummar da dakataccen sankaran Bauchi ta Tsakiya Sanata Abdul Ahmed Ningi, basu da wakili a majalisar dattawan kusan tsawon watanni uku, a dan haka akwai buƙatar a janye matakin dakatarwar ga Ningi, kasancewar akwai take hakki a cikin lamarin.

Continue Reading

Trending