Manyan Labarai
Ba’amurkiya da masoyin ta sun hada cinkoso a kasuwar Sabon Gari

Masoyan biyu sun dai kai ziyara ne kasuwar Muhammdu Abubakar Rimi dake sabon Gari a jihar Kano a yau Alhamis domin yin siyayyar kayan auren na su.
Ba Amurka Janine Sanchez mai shekaru 46 da haihuwa yar asalin jihar Carlifonia dake can kasar ta Amurk wadda ta yi tsaiwar daka kan cewar sai ta auri Sulaiman Isah Panshekara mai shekaru 23 da haihuwa wanda suka hadu a shafin sada zumunta na instgarm, kuma abun mamakin shi ne duk kokarin da mahukunta da sauran al’umma ke yin a ankarar da shi Sulaiman din kan illar aurar baturiyar ta yi burus da kalubalantar da ake yi mata na biyo sahibin na ta har garin Panshekara dake karamar hukumar Kuimbotso a jihar Kano.
Sai dai kuma a yau dinnan kasuwar ta Sabon Gari ta na tsaka da ciki sai masoyan suka bayyana a kasuwar domin yin siyayyar kayayyakin auren su lamarin da ya dau hankalin yan kasuwar da masu siyayya wanda kallo ya koma kan su lamarin da ya janyo siyayyar ta gagare su saboda yan hoton selfie da masoyan biyu.
Sakamakon cincirindon al’ummar zuwa yanzu ba a iya kayyade iya adadin mutanen da suka nuna bukatar su domin daukar hoto da masoyan ba wanda ya janyo siyayyar kayan auren ta gagara sai kai musu kayan a kayi har ofishin sarkin kasuwar.
Mun kuma zanta da sakataren sarkin kasuwar ta sabon gari, Sulaiman Adamu Indabo wanda ya ce” Mune muka kai su ofishin mu domin yawon mutanen ya kai yawan das ba za a iya iyakance sub a saboda farin jinin masoyan da suke shirin angon cewa”.
Mun kuma yi kokarin jin ta bakin masoyan amma hakar mu bai cimma ruwa ba.

Manyan Labarai
DSS sun kama Emefele bayan dakatar dashi daga Gwamnan banki

Rahotanni na cewa jami’an tsaro na farin kaya DSS sunyi awon gaba da Godwin Emefele, sa’a guda bayan Shugaban kasa Asuwaju Bola Ahmad Tinubu ya dakatar dashi daga Gwamnan babban banki.
Tun abaya dai an zargi Emefele da hannu wajen gurgunta tattalin arzikin kasa, baya ga zargin sa, da hannu wajen tabarbarewar tsaro.

Manyan Labarai
Da na hadu da kwankwaso da sai na mare shi – Ganduje

Tsohon Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje yace da sun hadu da kwankwaso da akwai yiyuwar ya mare shi, a fadar shugaban kasa.
Tsohon Gwamnan ya bayyana Hakan ne yayin wata ganawa da gidan television na channels, yayin da yake martani Kan ganawar shugaban kasa Asuwaju Bola Ahmad Tinubu da Kuma jagoran jam’iyyar NNPP Sanata Rabiu Musa Kwankwaso a yammacin wannan juma’a.
” Nasan yana gidan Amma bamu hadu ba, da mun hadu akwai yiyuwar na kwada masa Mari” inji Ganduje.
Idan za’a iya tunawa dai kwanakin baya shugaban kasa Asuwaju Bola Ahmad Tinubu yayi wata ganawa da kwankwaso, lamarin da aka jiyo tsohon Gwamnan na korafi cewa ba’a Yi musu adalchi ba, Koda dai a wancan lokaci, Ganduje ya musanta, ta bakin tsohon kwamishinan yada labarai Muhammad Garba, inda yace ba muryar Ganduje bace.
Wannan dai na zuwa ne a Gabar da gwamnatin Kano ke cigaba da rushe wuraren da tayi zargin gwamnatin baya ta Abdullahi Umar Ganduje ta cefanar ba bisa ka’ida ba.

Manyan Labarai
Gargadin Gwamnatin Kano Kan masu kaya a wuraren gwamnati

Gwamnatin jihar Kano ta gargadi dukkanin masu kaya a wuraren da tayi zargin gwamnatin baya ta cefanar ba bisa ka’ida ba, dasu kwashe kayan su cikin gaggawa.
Cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin Dakta Abdullahi Baffa Bichi ta fitar ta bayyana cewa, dukkanin masu kaya a shagunan da aka gina a jiki ko cikin makarantu, Maƙabartu, Asibitoci, Masallatai, gefen badala, Filayen ma’aikatu, Filayen wasanni da sauran wuraren shakatawa mallakin gwamnati da cewa suyi gaggawar kwashe dukkanin kayan su dake cikin shagunan da aka gina a waƴannan gurare ba tare da ɓata lokaci ba.

-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Manyan Labarai3 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai3 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi4 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai3 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya1 year ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Nishadi4 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai3 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano