Connect with us

Labarai

GWAMNATIN JIHAR KADUNA TA YUNKURO.

Published

on

Kwamishinan Ilimn Kimiyya da Fasaha na Jihar Kaduna, Alhaji Jafaru Sani, ya bayyana cewa, Gwamnatin Jihar Kaduna nan ba da jimawa ba za ta ci gaba da daukar malaman firamare a jihar. Kwamishinan ya bayyana haka ne a yayin da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa dake Kaduna.

Jafaru Sani ya ce, ” yanzu haka Hukumar Ilimi ta Bai daya ta kammala duk aikin daukar malaman firamare kashi na farko, wanda bayan jarrabawa da ganawa, da tantancewa, an samu nasarar daukar malamai 11,395 cikin malamai 25,000 da za a dauka.

Yanzu haka wadannan malaman an tura su kananan hukumomi da makarantun da za su koyar”

Sannan game da ci gaba da daukar sauran cikon malaman, kwamishinan ya bayyana cewa, nan ba da jimawa ba za su ci gaba da wannan aiki na daukar malaman firamare har sai an samu kwararrun malamai 25,000 da Gwamnatin Jihar ke son ta dauka.

Ya ci gaba da bayyana cewa, “Gwamnatin Jihar Kaduna za ta dauki kwararrun malamai guda 25,000 don haka yanzu bayan an tace, an tankade mun samu nasarar daukar malamai 11,395, kuma duk an tura su inda za su yi aiki. Bayan haka, muna da takardun masu neman aikin koyarwa akalla 19,000 a kasa nan ba da jimawa ba za mu yi masu jarrabawa don cike gurbin 25,000 din da muke son dauka. Sannan za a ci gaba da daukar malaman firamare har sai ya zamana kowane malami yana karantar da daliban da ba su wuce 40 a aji ba,kwamishinan ya kara da bayyana cewa, “Kamar yadda aka sani a wannan daukar malaman, mun karbi takardun neman aiki na sama da mutum 40,000, muka tantance muka rairaye muka fitar da sama da mutum 25,000 da suka zauna jarrabawar. Sannan kuma sama da mutum 15,000 suka sami nasarar cin jarrabawar.  Bayan nan kuma wurin ganawa da kara tantancewa muka sami malamai 11,395 wadda yanzu haka an tura su makarantun da za su koyar”.

Haka kuma game da sabon tsarin albashi, kwamishinan ya ce, “Mun yi kudurin fara biyan albashi da sabon tsarin albashi a watan da ya gabata, amma saboda rashin kammala aikin daukar sababbin malaman nan, shi ya sa muka bari sai an kammala duka,yanzu haka muna sa ran duk ranar da za a fara biyan sababbin malaman firamaren da aka dauka, za a fara da sabon tsarin albashi kamar yadda aka yi alkawari, kuma wannan zai hada har da tsofaffin malamanmu”.

Labarai

Zamu yi aiki kafaɗa da kafaɗa da ƴan Jarida – Hukumar Zaɓe ta Kano

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSEC, ta sha alwashin aiki kafaɗa-kafaɗa da ma’aikatan Jarida, musamman ma da zaɓen ƙananan hukumomin jihar nan 44 da ke tafe.

Sabon shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan Manumfashi, ne ya bayyana hakan, yayin ziyarar da tawagar ƙuniyar matasan ƴan Jarida, ta Kano Youth Journalist Forum, suka kai masa a ofishin sa yau Alhamis, yayin da ya shafe kwanaki huɗu da kama aiki.

Ya kuma ce, za su yi aiki da ma’aikatan Jarida musamman ma yayin gudanar da ayyukan zaɓen ƙananan hukumomin Kano 44, da ke tafe, domin wayar da kan al’umma da ma samun nasara yayin zaɓen da ma bayan sa.

Farfesa Manumfashi, ya kuma ƙar da cewa, akwai buƙatar kowa ya bayar da tasa gudummawar a harkar zaɓe, domin kuwa yanzu haka suna ci gaba da aiki wajen shirya zaɓen ƙananan hukumomin.

Da yake nasa jawabin shugaban ƙungiyar matasa ƴan Jaridar ta jihar Kano Musa Zangina Adam, ya ce sun kai ziyarar ne, domin su ƙulla alaƙar aiki a tsakanin su da hukumar, bisa yadda kowanne ɓangare yake buƙatar juna, tare kuma da bayar da gudunmawar da ya kamata.

Zangina, ya kuma ce a shirye ƙungiyar su take wajen ci gaba da bibiyar al’amuran da suka shafi al’umma, tare da nusar da mahukunta dan ganin an wadata su da kayayyakin more rayuwa.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Trending