Connect with us

Labarai

An tono wata gawa da aka bunne a Kano

Published

on

Tun da fari dai Babbar kotun shari’ar Muslunci ce mai zaman ta a  kofar Kudu ce karkashin mai shari’a Ustazu Ibrahim Sarki Yola, ta yi umarnin a yiwa gawar sutura kasancewar hukumar Hizba ta roki kutun ta yiwa asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano Umarnin su bayar da gawar wani mai suna, Abdullahi Obinwa, inda a nan ne aka samu akasi aka musanya gawar da ta wani dan kabilar Ibo mai suna Basil Ejensi, bayan kuma ya cika umarnin kotun da kwanaki bakwai da binne shi.

Sai dai wasu ‘yan kabilar Ibo suka garzaya kotun ta mai shari’a Ustazu Ibrahim Sarki Yola, suka yi roko a gaban kotun cewar anyi musu musayar gawa domin haka kotun ta yi umarni a kwakulo gawar da ta bayar da damar binewa kwani bakwai da suka gabata domin dai tasu ce bata wadanda suka nema ba tun da fari.

Bayan jin kowanne bangare mai shari’a Ustazu Ibrahim Sarki Yola, ya bayar da wani umarnin cewar a samu rakiyar jami’an tsaro zuwa makabartar domin tono gawar mai kwanaki bakwai a bunne ta a waccan makabartar ta unguwar Gandun Albasa dake Karamar Hukumar Birnin Kano, da yammacin ranar Litinin dinnan,

Harma bayan kwakulo gawar daga kabarinta ankuma damkata ga Lauyan gawar Masalinas Duru, harma lauyan ke cewa” Hukuncin kotun ya yi mana dadi sakamakon an bamu gawar mu”.

Shima limamin da ya sallaci gawar Malam Aminu Ahmad Adam, ya ce” Kuskure ne an riga an yi shi kuma babu wanda ya wuce ya aikata shi”.

Sai dai Jami’in hukumar Hizba mai lura da Makabarta, Malam Jamilu, wanda su ne suka yi kara ta farko ya ce” Na yi mamaki  game da wannan lamarin da ya kasance”.

Suma wasu da suka ganewa Idanuwansu yadda Ka hako gawar sunce har da jami’an tsaro a rakiyar kuma a gaban su aka kwakulo gawar sannan aka daura shi a gadon asibiti kuma tuni ‘yan uwan sa suka tafi da shi.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending