Manyan Labarai
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano

Kwamandan ‘yan sinitir na Bigilante a karamar hukumar Birni, Idris Adamu Sharada, ya ja hankalin masu sana’ar sayar da Gawayi a karamar hukumar, da su yi taka tsantsan da wani sabon salon damfara da wadan su ba ta gari su ke yiwa masu sana’ar gawayin.
Idris Adamu Sharada ya yi jan hankalin ne, a lokacin da su ka samu nasarar kama daya daga cikin wadanda a ke zargi da irin wannan damfarar, ta hanyar zuwa da mota a loda musu gawayin da sunan za su sauke, su kuma dawo su kara sannan kuma su biya kudin gaba daya.
Ya kuma ce” Sun dade suna bibiyar mutanen sakamakon korafe-korafen da al’umma suke yi a kansu, inda a wannan lokacin suka samu nasarar kama daya daga cikin su. Mun samu rahoton cewa wanda a ke zargin ya karbi buhun Gawayin masu tarin yawa daga wurin mutane daban-daban”.
Wakilin mu Aminu Ahmad Abbas, ya rawaito cewa yanzu hakan wanda ake zargin ya na hannun jami’an tsaro domin fadada buncike da kuma daukar mataki na gaba.

Manyan Labarai
Shekaru 63 na Nigeria:- Jawabin Gwamnan Kano

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya buƙaci shugabanni da saura al’umma da suyi koyi da tsaffin shugabannin da suka gabata wajen kawowa ƙasar nan ci gaba da zaman lafiya musamman a irin wannan lokaci.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana hakan ne a yau yayin da yake jawabi kan cikar ƙasar nan shekara 63 da samun kyancin kai daga hannun turawan mulkin mallaka.
Gwamna Abba ya kuma ce la’akari da yadda ake tunawa da tsaffin shugabanni wajen ciyar da ƙasar nan gaba ya kamata su shugabannin yanzu suyi koyi da su.
Ka zalika ya ƙara da cewa ya kamata shugaban ni su tabbata sun yiwa al’umma abin da suke buƙata domin tabbatar adalci.
Gwamnatin tace zata ci gaba da gudanar da aikin ta kamar yadda ta tsara domin ciyar da Kano gaba.

Hangen Dala
Hukuncin Kaduna :- PDP za ta daukaka kara

Jam’iyyar PDP reshen jihar Kaduna ta yi watsi da hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ta tabbatar da zaben Gwamna Uba Sani na jam’iyyar APC, inda ta ce za ta garzaya kotun daukaka kara.
Alberah Catoh, Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar PDP ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Juma’a a Kaduna.
Catoh ya ce, wani nazari da lauyan PDP ya yi ya nuna cewa hukuncin bai cika wasu ka’idoji na tabbatar adalci ba.
Martanin ya zo ne sa’o’i bayan kotun da ke zamanta a Kaduna ta amince da nasarar zaben Sani.
Ya kara da cewa hukuncin bai dace da wasu dokoki da ka’idojin zabe ba.
Sanarwar ta kara da cewa, “Saboda haka jam’iyyar ta umurci lauyoyinta da su daukaka kara kan hukuncin da aka yanke a kotun daukaka kara da ke Abuja a cikin wa’adin da doka ta kayyade.”
Catoh ya kuma bukaci magoya bayan jam’iyyar PDP a fadin jihar da su kwantar da hankalinsu tare da nuna kwarin gwiwarsu kan lamarin.

Hangen Dala
Abba ya biyawa Daliban Kano kudin makaranta

Abba Kabir ya biya kuɗin makarantar ɗaliban Jami’ar Bayero
Gwamnatin jihar Kano ta ce, ta biya kuɗin makarantar ɗaliban Jami’ar Bayero, waɗanda ba su samu damar biya ba, kimanin Naira Miliyan ɗari bakwai.
Sakataren hukumar bayar da tallafin ilimi ta jihar Kano, Hon. Kabir Getso Haruna ne, ya bayyana hakan a ranar Talata.
Yana mai cewa, “Yanzu haka Gwamnatin Kano, ta biya wa ɗalibai ƴan asalin jihar, dubu bakwai kuɗin makarantar”.
Ya kuma ce, “Daga yau Talata, dukkan ɗaliban, su tafi Jami’ar Bayero, tsangayoyin su, domin ƙarasa rijista na shekarar 2023, su ci gaba da karatu”. Inji Hon. Kabir Getso.

-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Manyan Labarai4 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai3 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi4 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai4 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya1 year ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Nishadi4 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai4 years ago
Ba’amurkiya da masoyin ta sun hada cinkoso a kasuwar Sabon Gari