Connect with us

Manyan Labarai

Sabuwar damfarar da ta fito a Kano

Published

on

Kwamandan ‘yan sinitir na Bigilante a karamar hukumar Birni, Idris Adamu Sharada, ya ja hankalin masu sana’ar sayar da Gawayi a karamar hukumar, da su yi taka tsantsan da wani sabon salon damfara da wadan su ba ta gari su ke yiwa masu sana’ar gawayin.

Idris Adamu Sharada ya yi jan hankalin ne, a lokacin da su ka samu nasarar kama daya daga cikin wadanda a ke zargi da irin wannan damfarar, ta hanyar zuwa da mota a loda musu gawayin da sunan za su sauke, su kuma dawo su kara sannan kuma su biya kudin gaba daya.

Ya kuma ce” Sun dade suna bibiyar mutanen sakamakon korafe-korafen da al’umma suke yi a kansu, inda a wannan lokacin suka samu nasarar kama daya daga cikin su. Mun samu rahoton cewa wanda a ke zargin ya karbi buhun Gawayin masu tarin yawa daga wurin mutane daban-daban”.

Wakilin mu Aminu Ahmad Abbas, ya rawaito cewa yanzu hakan  wanda ake zargin ya na hannun jami’an tsaro domin fadada buncike da kuma daukar mataki na gaba.

 

Manyan Labarai

Mun kama mutane 14 bisa zargin su kan kisan gillan da aka yi wa Mafarauta a Edo – Ƴan Sanda

Published

on

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta tabbatar da kama mutane 14 da ake zargi da hannu kan kisan da aka yi wa wasu Mafarauta kuma Hausawa ƴan Arewa a garin Uromi da ke jihar Edo.

Sufeton ƴan sandan kasar IGP Kayode Adeolu Egbetokun, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar na ƙasa ACP Olumuyiwa Adejobi ya fitar a ranar Juma’a.

Sanarwar ta ce, tuni Egbetokun ya bai wa mataimakin sa mai kula da babban sashin binciken manyan laifuka na rundunar DIG Sadik Abubakar, umarnin da ya ja ragamar bincike don gano sahihin abinda ya faru tare da ɗaukar matakin da ya dace akan al’amarin.

Idan dai ba’a manta ba, rahotanni sun bayyana cewar mafarautan sun baro birnin Fatakwal ne na jihar Ribas, suna kan hanyar su ta komawa Kano, don gudanar da bikin ƙaramar Sallah, suka gamu da wasu Ƴan Bijilante a garin Uromi da ke jihar Edo, lamarin da suka zarge su da cewa ƴan garkuwa da mutane ne bisa samun su da bindigar gargajiya duk kuwa da sun ce suna da lasisin bindigun.

A cewar jaridar Daily Trust, duk da haka ƴan bijilanten suka sakko da mutanen su aƙalla 27, daga motar dakon kaya ta Ɗangote, suna dukan su, har su ka ƙone kusan mutane 16 daga cikin su, ko da dai wani da ya tsira da ransa ya ce, mutane 20 aka kone, su biyar suka tsira, yayin da mutane biyu suke Asibiti.

IGP Egbetokun, ya kuma ce jim kaɗan da faruwar lamarin ne jami’an rundunar ƴan sanda ta jihar Edo, suka baza koma tare da cafke mutane 14 da ake zargi da hannu kan lamarin, kuma yanzu haka ana faɗaɗa bincike akan batun.

Tuni dai ƴan ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’adama, da Ƴan Siyasa, da sauran al’ummar Najeriya, suke ta kiraye-kirayen ganin an ɗauki matakin da ya dace akan lamarin, don zama izina ga ƴan baya.

Continue Reading

Manyan Labarai

Hukumomin tsaro ku gaggauta ɗaukar matakin kama waɗanda suka yi wa Mafarauta kisan gilla a Edo – Barau Jibrin

Published

on

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattijai Sanata Barau Ibrahim Jibrin, ya ce za su tabbatar da cewa an yi adalci, akan waɗanda suka yi wa al’ummar Arewa kisan gilla a Uromi ta jihar Edo, kuma wadannan azzalumai ba za su tsira ba.

Sanata Barau ya bayyana hakan ne a zantawar sa da Freedom Radio, ya ce ya samu kiraye kiraye daga al’ummar yankin sa, da kuma ƴan Najeriya da dama game da mummunan kisan gillan da aka yi wa bayin Allah da basu ji ba basu gani ba a Jihar ta Edo.

“Ina Allah wadai da wannan ta’asa, kuma na yi tir da wannan kisan gilla da aka yi wa wadannan bayin Allah; ina kuma kira ga hukumomin tsaro da su gaggauta ɗaukar matakin kama wadannan azzalumai tare da tabbatar da cewa an hukunta su dai-dai da girman laifin da suka aikata, “in ji Barau”.

A cewar sa, Najeriya ƙasa ce mai yalwar Ƙabilu da addinai daban-daban. Saboda haka, dole ne mu zauna lafiya da juna, mu rungumi juna a matsayin ‘yan uwa domin ci gabanbmu da zaman lafiyar mu.

“Zan kuma gabatar da ƙudiri a zauren Majalisar Dattawa kan wannan lamari “in ji Barau”

Ya kuma yi addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki ya jikan waɗanda suka rasa rayukansu, ya ba su Aljannatul Firdaus. Allah ya ba iyalansu hakuri da juriya.

Continue Reading

Manyan Labarai

Gwamnatin jihar Edo ki gaggauta binciko waɗanda suka yi wa ƴan Arewa kisan gilla – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam da wayar da kan jama’a da kuma tallafawa mabuƙata a Najeriya, ta yi Allah wa-dai da kisan gillan da aka yi wa wasu mafarautan su kusan 16 a jihar Edo, waɗanda suke kan hanyar su ta zuwa Arewa daga jihar Rivers.

Daraktan ƙungiyar ta Awareness for Human Rights and Charity Foundation na ƙasa Kwamared Auwal Usman ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM a ranar Juma’a,

Ya kuma yi kira ga gwamnatin jihar Edo da ta gaggauta gudanar da bincike wajen ganin wadanda suka aikata rashin imanin, tare da yin adalci akan lamarin.

Daily Trust ta rawaito cewa wasu ɓata gari ne su ka damƙe waɗanda abin ya shafa a Uromi da ke karamar hukumar Esan ta Arewa maso Gabas ta Jihar Edo, inda su ka ga bindigogin farauta a motar da suke, sai kawai su ka yanke cewa ai masu garkuwa da mutane ne, inda suka kona su da ransu.

Lamarin dai ya jawo cece-ku-ce, inda ‘yan Najeriya da da ma ke zargin gwamnati da gazawa wajen dakile irin wannan ɗaukar doka a hannu.

“Duk waɗannan abubuwan da suke faruwa a ƙasa musamman ma arewacin Najeriya, laifin jami’an tsaro ne, shi ya sa al’amarin yake ci gaba da faruwa tunda matsalar tsaron nan ba yau ne farau ba, “in ji Auwal Usman”.

A cewar sa, gwamnati da jami’an tsaro sune suke da alhakin tsare rayuka da dukiyoyin al’umma, a don haka ya ce za su gurfanar da rundunar ƴan sandan Najeriya ƙara a kotu bisa wasarere da take yi da aikin ta na kare al’ummar ƙasar.

Tuni dai, Gwamnan jihar Edo Monday Okpebholo, ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan kashe wasu mafarauta da su ke kan hanyar su ta zuwa Arewa domin bikin Sallah.

Continue Reading

Trending