Connect with us

Lafiya

Wasu daga hudubobin juma’a a Kano

Published

on

Babban limamin masallacin Juma’a na Abdullahi Ibn Mas’ud dake unguwar Kabuga ‘yan Azara, Malam Zakariyya Abubakar ya bukaci mutane da su tashi tsaye wajen umarni da kyakkawan aiki da kuma hani da mummuna ta yadda al’ummar baki daya za ta samu tsira daga faruwar musifu da Annoba.

Malam Zakariyya Abubakar ya bayyana hakan ne ta cikin hudubar Juma’a daya gabatar yau a masallacin.

Ya kuma ce, “Hani da mummunan aiki da kuma umarni da kyakkawa, ibada ce wadda kowa zai iya yi gwargwadon ikon sa, musamman ma a wannan lokaci da ake samun yaduwar munanan ayyuka a tsakanin al’umma.”

Ya kara da cewa, “Ana gudanar da umarnin da kyakkawan da kuma hani da mummunan ta cikin sauki da nasiha, bawai da cin zarafi ko wulakanci ba.” Inji Malam Zakariya.

Limamin masallacin Juma’ar na Abdullahi Ibn Mas’ud, Malam Zakariyya Abubakar, ya kuma shawarci musulmi da su kasance masu jin tsoron Allah a cikin dukkanin al’amuransu.

 

Shi kuwa limamin masallacin juma’a na Sheikh Abubakar Mahmud Gumi dake garin Mariri a karamar hukumar Kumbotso, Malam Sunusi Adamu Birnin Kudu, ya ja hanakalin mawadata da su yi kyakkawan amfani da arzikin da Allah ya ba su wajen taimakawa mabukata domin samun guzuri zuwa lahira.

Malam Sunusi ya bayyana hakan ne a hudubarsa da ya gudanar yau juma’a a masallacin.

Ya na mai cewa, “Taimako tsakanin mawadata da masu karamin karfi, ya na taimakawa matuka wajen samar da kyakkyawar zamantakewa a tsakanin al’umma, dama kuma tunkude faruwar musifu daga dukiyar.”  A cewar Malam Birnin Kudu.

Daga karshe limamin ya kuma gargadi ‘ya’ya dangane da wajabcin yiwa iyayensu biyayya domin da cewa a duniya da kuma ranar gobe kiyama.

A nasa hudubar limamin masallacin juma’a na Umar Sa’id Tudun Wada dake gidan rediyo a yankin unguwar Tukuntawa a karamar hukumar birnin Kano, Gwani Fasihu Muhammad Dan Birni, ya yi kira ga wanzamai da su rinka sa ni tare da neman ilimi a kan bangaren yin shayi ga ‘ya’ya mata da suke yi wa wasu daga cikin su.

Gwani Fasihu Muhammad Dan Birni, ya yi wannan kiran ne a lokacin hudubar sallar juma’a na yau wanda ya gudana a masallacin.

Ya ce” wanzamai da su rinka zuwa neman sa ni kan yadda a ke gudanar da shayi ga ‘ya’ya mata maimakon su rinka yin ta kai tsaye domin hakan na illata ‘ya’ya mata musamman.

Lafiya

Ku rinƙa ziyartar Asibiti ana muku gwaje-gwajen fitsari da Jini domin sanin halin da ƙodar ku take ciki – Likita

Published

on

An shawarci al’umma da su rinƙa ziyartar Asibiti akai akai wajen duba lafiyar su, ta hanyar yin gwaje-gwajen fitsari da jini domin sanin halin da kodar su ke ciki.

Dakta Muhajid Sunusi Rabi’u ne ya bayyyana hakan yayin ganawarsa da Dala FM, lokacin da suke aikin gwaje-gwajen fitsari da jini, kyauta a ɗaya daga cikin makarantu masu zaman kan su a nan Kano.

Dakta Mujaheed ya kuma ce sun gudanar da aikin ne a wani ɓangare na bikin ranar ƙoda ta Duniya, wadda aka ware duk ranar Alhamis ta mako na biyu na kowanne watan Maris domin gudanar da bikin ranar.

Continue Reading

Lafiya

Za’a yiwa kusan yara miliyan 3 rigakafin cutar shan Inna a Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano tace kusan Yara miliyan 3 za’ayiwa rigakafin cutar shan inna a kananan hukumomin jihar nan 44, duba da samun ɓurɓushinta da kaso 65, a jihar ta Kano.

Kwamishinan lafiya na jihar Kano Dakta Abubakar Labaran Yusuf ne ya bayyana hakan yayin ƙaddamar da rigakafin cutar shan innar a yau Alhamis, wanda za’a kwashe kwanaki 4 ana gudanarwa a Kano.

Dakta Abubakar Labaran ya ce duba da shigowar zafin akwai buƙatar al’umma su kula da alamomin cutar sankarau, duk da gwamnati ta yi shirin bayar da agajin gaggawa, kamar yadda tashar Dala FM Kano ta rawaito.

Ma’aikatar lafiyar ta jihar Kano dai ta ce za’a ci gaba da gudanar da sauran rigafin, domin bai wa yaran jihar Kano kariya daga cututtuka masu yaɗuwa.

Continue Reading

Lafiya

Dokar tilasta gwajin lafiya kafin aure ta tsallake karatu na biyu a majalisar dokokin Kano

Published

on

Rahotanni na bayyana cewar majalisar dokokin jihar Kano, ta yi karatu na biyu a kan kudirin dokar tilasta wa masu niyyar yin aure yin gwajin cutar kanjamau, da na cutar hanta da kuma duba kwayoyin jini wato Sikila, gabanin daura aure.

Ɗan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Takai, Hon.Musa Ali Kachako, shin wanda ya kawo kudirin dokar, ya bayyana cewa, jihar Kano na fama da matsalolin lafiya daban-daban da suka hada da cutar kanjamau saboda mutane kan yi aure ba tare da an duba lafiyarsu ba, hakan ne ma ya sa ya kai ƙudirin.

Kachako, ya ce, ƙudirin dokar idan har aka amince da shi, zai ceci rayuka da dama tare da dakile yaɗuwar cututtuka masu barazana ga rayuwar al’umma, kamar yadda jaridar Kadaura24 ta rawaito.

Da yake nuna goyon bayansa kan ƙudirin Ɗan majalisa Hon. Aminu Sa’ad, mamba mai wakiltar mazabar Ungogo, ya ce, jihohin Jigawa, Katsina da Kaduna sun zartar da irin wannan kudiri domin magance kalubalen kiwon lafiya da suke fuskanta.

Ya ce tilas ne Kano da ke da yawan al’umma a kasar nan ta zartar da kudirin dokar, domin kare lafiyar ‘yan jiharta ta hanyar samar da gwaje-gwaje kafin aure domin dakile yaduwar cututtuka, kamar cutar hanta, da sauran cututtuka.

Continue Reading

Trending