Connect with us

Manyan Labarai

An yi biyan bashi da budurwa a Kano

Published

on

A karamar hukumar Bichi kuwa wata dambarwa ce ta barke, inda ake zargin wani uba yayi biyan bashi da ‘yar sa a kan kudi naira dubu tamanin.

Budurwa mai suna Rahma Abdurrahman ‘yar shekaru 16 a duniya, inda ta bayyana mana cewa Mahaifinta sun rabu da mahaifiyar ta, kuma yanzu tsawon shekara 7 kenan da mahaifin ya rabata da mahaifiyar ta, inda ya kai ta garin Zaria, babu makarantar Allo balantana ta boko. Hassalima babban aikin ta safe zuwa dare shi ne yin noman masara da shinkafa.

Ana wannan zaman ne sai mahaifin ya nemi bayar da ita aure gun wani da yake binsa bashin naira dubu tamanin a don haka zai yi biyan bashi da ita.

A yayin da ake tsaka da shirye-shiryen shagalin wannan aure ne sai Rahma ta gudo zuwa Bichi wurin mahaifiyar ta.

Wane tudu wane gangare shi kuma maihaifin na ta sai yayi tattaki daga Zaria zuwa Bichin, ya kuma shigar da karar mahaifiyar Rahman a wurin jami’an tsaro cewa ta sace masa ‘yar sa inda akai zargin sun yi musu sulhu, suka yi sulhu a tsakanin su, inji mahaifiyar Rahman mai suna Sahura Halilu, amma ta ce daga baya mahaifin Rahman wato tsohon mai gidan nata, ya sake shigar da ita kara a gaban kotun shari’ar musulunci dake garin Bichi, kan wancan zargin dai na cewar ta sace masa yarinya.

Har ila yau, mahaifiyar Rahma ta sheda mana cewa,tun bayan da mahaifin su Rahma ya tattara yaranta ya tafi dasu kuma koda ta je zuwan farko domin duba halin da suke ciki, sai ya fada mata cewa kada ta kuskura ta kara zuwa inda ya ke shi da ‘ya’yan sa.

Kazalika ya yi mata ikrarin cewa akwai wani kulumboto da ya yi wanda har abada ba zata taba yin aure ba.

Yanzu haka dai tuni wata lauya mai fafutukar kare hakkin al’umma, Barista Hadiza Nasir Ahmad ta shiga wannan shari’a domin bayar da kariya ga wannan budurwa da mahaifiyar ta, Barista dai ta ce wannan aure da ake shirin yi ya saba da tsari irin na addinin Islama.

Shi ma a nasa bangaren mahaifin wannan Budurwa Alhaji Abdurrahman ya ce ko kadan ba haka wannan zance yake ba, domin kuwa bashi da labarin auren biyan bashin game da ‘yar tasa, ya dai san cewa a baya ya yi shirin yi mata auren zumunci amma ba auren bashi ba bane.

Dangane da ikrarin mahaifiyar Rahma kuwa na cewa Malam Abdurrahman din ya yi wani kulumboto, ya ce shi fa dogaron sa Allah.

Manyan Labarai

Gwamnatin Kano ta kulle wata makaranta mai zaman kan ta a jihar

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta rufe wata makaranta mai suna Golden Crown International School a jihar, da ke yankin Sabon gari, bisa zargin an fake da sunan makarantar ana haɗa magani mara inganci mai-makon koyar da karatu a ciki.

Shugaban kwamitin yaki da miyagun ƙwayoyi da ƙwacen waya na jihar Kano General Gambo Mai Aduwa Mai ritaya, ne ya bayyana hakan, a lokacin da Kwamitin ya kai wani sumame da karfe uku da rabi na daren jiya Talata.

Rahotanni sun bayyana cewa makarantar tana kan titin Zungero da ke cikin ƙaramar hukumar Fagge a jihar Kano, wanda bayan samun bayanan sirri aka ɗauki matakin kulle ta.

Mai Aduwa, ya ƙara da cewar tsarin gurin ta waje ya nuna makaranta ce amma kuma sai ake sarrafa magani da ake zargin ingancin sa da bai kai yadda ya kamata ba, tare da ajiye Allurai da kayan haɗa magani cikin ajujuwan mai-makon ɗalibai.

“Za mu faɗaɗa bincike akan al’amarin dan sanin matakin da za mu ɗauka na gaba, “in ji shi”.

Suma masu gadin gurin da muka zanta da su sun bayana cewar, aikin gadi kawai suke yi amma basu da masaniyar abubuwan dake gudana a cikin makarantar, da ake zargin ana sarrafa magani mara ingani da ajiye shi a muhalin da ake zargin bai yi dai-dai da tsarin doka ba.

Wakilinmu Abba Isah Muhammad ya rawaito cewa shugaban kwamitin ya ce, zai ci gaba da bibiyar guraren dake yin abubuwan da za su kawo koma baya ga harkokin lafiya, da ci gaban jihar Kano, musmman wajen yaƙi da miyagun ƙwayoyi da ƙwacen waya.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ƙaramar hukumar Tofa ta musanta zargin gididdiba burtalai a wasu garuruwan ta uku

Published

on

Ƙaramar hukumar Tofa ta musanta batun gididdiba burtalai a garuruwan Yanoko da Gajida da kuma Dindere, dukka a ƙaramar hukumar da ake zargin an siyarwa Manoma, domin suyi aikin Noma.

Shugaban riƙo na ƙaramar hukumar ta Tofa Abubakar Sulaiman Mai Rogo, ne ya bayyana hakan a daren jiya Laraba, lokacin da yake tsokaci kan koken da Fulani Makiyaya mazauna garuruwan suka yi, kan yadda suka zargi an gididdiba burtalai a yankunan su, an siyarwa wasu Manoma, domin suyi aikin Noma, lamarin da suka ce hakan barazana ce a gare su.

Mai Rogo, ya kuma ce ƙaramar hukumar ba ta da hannu wajen gididdiba burtalai a garuruwan, yana mai cewa ko da kansilolinsa daga zuwan su bai taɓa sanin wanda ya siyar da koda kuwa kunya ɗaya ba a cikin shugabancin sa na ƙaramar hukumar domin ayi Noma, haka shima bai siyar ba.

“Yanzu haka ana kan ɗaukar matakin doka akan waɗanda suka fitar da al’amarin, kasancewar maganar tana wajen ƴan sanda, kuma ana faɗaɗa bincike, “in ji shi”.

A ziyarar gani da Ido, da tashar Dala FM Kano, ta kai wasu daga cikin burtalan da aka yi zargin an siyarwa Manoman, ta iske yadda wasu mutane suke share guraren, kamar yadda suka shaida cewa waɗanda aka siyarwa ne suka basu aikin share wajen.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa, wannan na zuwa ne bayan da wasu Fulani Makiyaya mazauna garuruwan suka koka, bisa yadda suka ce an gididdiba burtalai a yankunan su, duk da wani manomi yace har takarda aka bashi bayan an siyar masa, lamarin da ya sa su cikin damuwa bisa yadda hakan ka iya sanyawa su rasa guraren da za su yi kiwon Shanun su.

Continue Reading

Manyan Labarai

Gididdiba burtalan garuruwan mu da akayi ka iya haifar mana da barazana – Fulani mazauna ƙaramar hukumar Tofa

Published

on

Fulani Makiyaya na garuruwan Yanoko, da Gajida, da kuma garin Dindere da ke ƙaramar hukumar Tofa, sun koka tare da neman ɗaukin mahukunta, bisa yadda suka ce sun wayi gari da ganin wasu mutane tare da yanka burtalan garuruwan su,

Fulanin sun ce zargi ya nuna yadda aka godiddiba burtalan inda aka siyarwa da wasu shafaffu da mai, lamarin da suka ce hakan babbar barazana ce a gare su, kasancewar babu wajen da za suyi kiwon shanun su.

A zantawar Dala FM Kano, da shugaban ƙungiyar Fulani Makiyaya reshen ƙaramar hukumar Tofa, ta Gan Allah, Mallam Ahmad Shehu, ya ce gididdiba burtalan ka iya haifar musu da gagarumar matsala a rayuwa, a dan haka ne ma suke kira ga gwamnatin Kano da ta kawo musu ɗauki.

Alhaji Mamuda mazaunin Dawakin Tofa, na ɗaya daga cikin waɗanda aka yankarwa burtalin a yankin Dindere, aka kuma siyar masa, ya ce wasu ne suka siyar masa kuma an bashi takarda hakan ya sa har ya fara aiki a wajen

Wakilin dagacin garin Dindere Isah Sulaiman ya ce, lamarin yaje ga ofishin hakimin Tofa, a dan haka ne muka zanta da Turakin Tofa, Alhaji Sunusi Abubakar Tofa, kuma wakilin Makaman Bichi hakimin Tofa Alhaji Dakta Isyaku Umar Tofa, ya ce sun san da al’amarin ana ci gaba da ɗaukar mataki, kuma masarautar yankin bata bai wa kowa damar yankar burtalin ba, ko da kuwa mai unguwar Yalwal Rimi da ke garin Dindere da akace shima ya yanki burtalin.

Al’amarin gididdiba burtalin dai wasu sun danganta shi da shugabancin ƙaramar hukumar Tofa mai ci a yanzu, a dan haka ne muka yi duk mai yiyuwa wajen ji daga shugaban riƙo na ƙaramar hukumar Abubakar Sulaiman Mai Goro, sai dai bai samu damar ɗaga wayar mu ba, kuma mun aike masa da saƙon karta kwana sai dai har wannan lokaci ba muji daga gareshi ba.

Continue Reading

Trending