Connect with us

Labarai

Dalilan da ya sa mata suka wuce maza a karatun kur’ani -Farfesa Isa Hashim

Published

on

Farfesa Isa Hashim ya ce mata sun fi maza basira, juriya da hakuri a bangen karatun addini, wanda hakan ya sanya ko a yaushe matan ke wuce maza a lokutan saukar karatun alkur’ani mai girma a makarantun Islamiyyu.

Farfesa Isah Hashim wanda shi ne Jarman Kano a yanzu, ya bayyana hakan ne a lokacin saukar karatun alkur’ani mai girma na dalibai maza 25 da Kuma mata 37 ciki harda wadda ta haddace alkur’anin a makarantar Imamu Dalhatu Islamiyyu sorondinki wanda wannan shi ne karo na 3 da saukar da a ka yi a cikin karshen makon da ya gaba.

Ya Kuma ce” Basirar da juriyar da kuma hakuri na daga cikin manyan sharudan samun ilimi, wanda kuma da yawa daga cikin maza basu da su, sabo da yadda suke shagaltuwa wajen sauke nauyin da Allah ya dora musu na gwagwarmayar nemo abun bukatar yau da kullum”. Inji Jarman Kano.

A nasa bangaren shugaban makarantar Habibu Abbas ya ce” Kamata ya yi mazan su rinka mayar da hankali a kan karatun su musamman ma a lokacin da suke matakin kuruciya, tun kafin su girma nauyin rayuwa ya yi musu yawa”.

Ita kuwa dalibar guda daya tilo da ta samu haddar alkur’anin daga cikin dalibai 65 din da suka sauke, Fari’atu Yusuf Yakubu, ta ce “duk da cewar haddar daga Allah ne amma, hakuri da juriyar sune sirrin samun haddar ta wa”. Inji Fari’atu.

Wakilin mu Ibrahim Abdullahi Sorondinki ya rawaito cewa, daga cikin daliban akwai wadanda suka fara haddar inda suke kan matakin izufi talatin a halin yanzu.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending