Connect with us

Labarai

Dalilan da ya sa mata suka wuce maza a karatun kur’ani -Farfesa Isa Hashim

Published

on

Farfesa Isa Hashim ya ce mata sun fi maza basira, juriya da hakuri a bangen karatun addini, wanda hakan ya sanya ko a yaushe matan ke wuce maza a lokutan saukar karatun alkur’ani mai girma a makarantun Islamiyyu.

Farfesa Isah Hashim wanda shi ne Jarman Kano a yanzu, ya bayyana hakan ne a lokacin saukar karatun alkur’ani mai girma na dalibai maza 25 da Kuma mata 37 ciki harda wadda ta haddace alkur’anin a makarantar Imamu Dalhatu Islamiyyu sorondinki wanda wannan shi ne karo na 3 da saukar da a ka yi a cikin karshen makon da ya gaba.

Ya Kuma ce” Basirar da juriyar da kuma hakuri na daga cikin manyan sharudan samun ilimi, wanda kuma da yawa daga cikin maza basu da su, sabo da yadda suke shagaltuwa wajen sauke nauyin da Allah ya dora musu na gwagwarmayar nemo abun bukatar yau da kullum”. Inji Jarman Kano.

A nasa bangaren shugaban makarantar Habibu Abbas ya ce” Kamata ya yi mazan su rinka mayar da hankali a kan karatun su musamman ma a lokacin da suke matakin kuruciya, tun kafin su girma nauyin rayuwa ya yi musu yawa”.

Ita kuwa dalibar guda daya tilo da ta samu haddar alkur’anin daga cikin dalibai 65 din da suka sauke, Fari’atu Yusuf Yakubu, ta ce “duk da cewar haddar daga Allah ne amma, hakuri da juriyar sune sirrin samun haddar ta wa”. Inji Fari’atu.

Wakilin mu Ibrahim Abdullahi Sorondinki ya rawaito cewa, daga cikin daliban akwai wadanda suka fara haddar inda suke kan matakin izufi talatin a halin yanzu.

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending