Connect with us

Manyan Labarai

Masu cin Beraye sun bayyana a Kano

Published

on

A yayin da masana lafiya ke gargadin mu’amala da Beraye domin gujewa kamuwa da cutar Lassa sakamakon cutar an gano cewa Beraye ne ke hadda sa cutar ga bil Adama.

Sai gas hi wasu mutane da suka mayar da Beraye naman cimakar su a cikin abincin sun a yau da kulum.

Mutanen wanda suka ya da zango a cikin garin Rogo dake karamar hukumar sun ce cikin Berayen da suke ci babu wanda ya taba samun wata matsala ga lafiyar su, duk da cewa cutar Lassa ta samo asali ne ga Beraye.

Michel Joseph da shi da iyalai da ‘yan uwansa wanda suka sami masauki a cikin garin Rogo ya ce” Mu masu kama Beraye ne kuma ba mu san irin Berayen ba kuma bamu samu matsala da sub a, domin kuwa abincin mu ne Bera muna kama su kuma muna cin su, duk cikin mu babu wani wanda ya samu wata cuta gamunan garau muna zaune har kwado muna ci”.

Likitoci suna cewa a jikin Beraye a ke samun cutar Lassa, ba kwajin tsoron cutar Lassa?

“Berayen da a ka ce suna kawo cutar mu a yankin mu babu wani Bera mai cutar, mu da muke ci har yanzu ba mu samu wata matsalaba, mu (27) wanda muke cin Berayen mu yi miya da su mu zuba a abincin mu har yanzu babu wata matsala da muka fuskanta”.

Yanzu in na kawo muku Bera za ku siya?

“Ba ma siya muna amfani da tarkon mu kama, ko ka kawo ma nan aka ba za mu siya ba, wanda muke kamawa shi muke ci muke kaoshi”.

Wane irin tarko ku ke amfani ku kama Berayen?

“Mun hada tarko mu saka a kan hanyar Berayen ba tare da wata matsala ba, ka gam un zo garin Rogo mun zauna mun samu abun da muke bukata yanzu muna saka tarko sai ka gam un kama Beraye da yaw aba tare da wata matsala ba, kuma mu gyara mu ci ko ciwon kai ba ma yi”.

A na baku hadin kai yayin kama Berayen?

“ Eh bamu da wata matsala domin mahukunta sun san da zaman mu kuma in zamu shiga cikin gona mu kama zamu shiga ba tare da wata matsala ba, in kuwa k ace mu fita daga gonar Raken ka sai mu fita tunda har yau ba wanda ya ce mun yi masa satar rake a cikin gonar sa”. Inji Michel Joseph a cikin tattaunawar mu da shi”.

Ga cikaken hirara tamu da shi.

Duk da annobar cutar Lassa sai gashi wasu mutane da sun bayyana a Kano suna shan dabgen Beraye.

Manyan Labarai

Gididdiba burtalan garuruwan mu da akayi ka iya haifar mana da barazana – Fulani mazauna ƙaramar hukumar Tofa

Published

on

Fulani Makiyaya na garuruwan Yanoko, da Gajida, da kuma garin Dindere da ke ƙaramar hukumar Tofa, sun koka tare da neman ɗaukin mahukunta, bisa yadda suka ce sun wayi gari da ganin wasu mutane tare da yanka burtalan garuruwan su,

Fulanin sun ce zargi ya nuna yadda aka godiddiba burtalan inda aka siyarwa da wasu shafaffu da mai, lamarin da suka ce hakan babbar barazana ce a gare su, kasancewar babu wajen da za suyi kiwon shanun su.

A zantawar Dala FM Kano, da shugaban ƙungiyar Fulani Makiyaya reshen ƙaramar hukumar Tofa, ta Gan Allah, Mallam Ahmad Shehu, ya ce gididdiba burtalan ka iya haifar musu da gagarumar matsala a rayuwa, a dan haka ne ma suke kira ga gwamnatin Kano da ta kawo musu ɗauki.

Alhaji Mamuda mazaunin Dawakin Tofa, na ɗaya daga cikin waɗanda aka yankarwa burtalin a yankin Dindere, aka kuma siyar masa, ya ce wasu ne suka siyar masa kuma an bashi takarda hakan ya sa har ya fara aiki a wajen

Wakilin dagacin garin Dindere Isah Sulaiman ya ce, lamarin yaje ga ofishin hakimin Tofa, a dan haka ne muka zanta da Turakin Tofa, Alhaji Sunusi Abubakar Tofa, kuma wakilin Makaman Bichi hakimin Tofa Alhaji Dakta Isyaku Umar Tofa, ya ce sun san da al’amarin ana ci gaba da ɗaukar mataki, kuma masarautar yankin bata bai wa kowa damar yankar burtalin ba, ko da kuwa mai unguwar Yalwal Rimi da ke garin Dindere da akace shima ya yanki burtalin.

Al’amarin gididdiba burtalin dai wasu sun danganta shi da shugabancin ƙaramar hukumar Tofa mai ci a yanzu, a dan haka ne muka yi duk mai yiyuwa wajen ji daga shugaban riƙo na ƙaramar hukumar Abubakar Sulaiman Mai Goro, sai dai bai samu damar ɗaga wayar mu ba, kuma mun aike masa da saƙon karta kwana sai dai har wannan lokaci ba muji daga gareshi ba.

Continue Reading

Manyan Labarai

Bama goyon bayan ƙirƙiro ƴan sandan jahohi dan ba zai haifar da Ɗa mai ido ba a ƙasa – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Universal Declaration of Human Rights, ta ce akwai buƙatar duba na tsanaki gabanin sahale ƙirƙirar ƴan sandan jahohi, domin gujewa abinda ka je ya dawo.

Daraktan ƙungiyar a nan Kano Kwamared Umar Sani Galadanci, ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, a yau Talata.

Galadanci, ya kuma ce duba da a mafi yawan lokuta ake samun baragurbi a harkar samar da taro, kamata ya yi a wadata jami’an tsaron da ake da su da kayan aiki na zamani, ta yadda za’a ƙara musu Gwiwa akan aikin su.

“A ɓangaren ƙungiyar mu bama goyon bayan samar da ƴan sandan jahohi, domin hakan ka iya haifar da koma baya; kuma ba zai haifar da Ɗa mai ido ba a sassan ƙasar nan, “in ji shi”.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa Kwamared Umar Sani Galadanci, ya ƙara da cewa akwai buƙatar gwamnatin tarayya da ta jahohi, su kula da al’ummar su tare da samar musu kayayyakin more rayuwa, dan rayuwar su ta tafi yadda ya kamata.

Continue Reading

Manyan Labarai

Mutane uku sun rasu yayin ciro Waya a cikin Masai da ceto mutum ɗaya a Kano – Hukumar Kashe Gobara 

Published

on

Hukumar kashe Gobara ta jihar Kano, ta tabbatar da mutuwar wasu mutane uku, ciki har da Uba ɗan sa, a unguwar Ƴar Gwanda da ke ƙaramar hukumar Tsanyawa a jihar Kano.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar kashe gobarar PFS Saminu Yusuf Abdullahi, ne ya bayyanawa gidan rediyon Dala FM, faruwar lamarin a daren jiya Lahadi.

Tunda fari dai mutum na farko mai suna Mallam Ɗan Juma mai laƙabin Black, wayar sa ce ta faɗa a cikin Masai, ya shiga domin ya cirota, sai dai gaza fitowar sa ke da wuya sauran mutane ukun suka bishi domin ceto shi lamarin da suma suka gaza fitowa.

Sauran mutane ukun akwai ɗan mutumin mai suna Ibrahim Ɗan Juma mai shekaru 35, sai na ukun mai suna Aminu T Gaye, da na huɗu mai suna Abbas Alhassan, ɗan shekara 28, amma shi an ciroshi a raye.

PSF Saminu Yusuf, ya kuma ce bayan faruwar lamarin ne jami’an su, suka ceto mutum na ƙarshe a raye, amma ukun farko basa cikin hayyacin su baki daya.

Ya ƙara da cewa tuni jami’an nasu suka miƙa mutanen a hannun jami’in hukumar ƴan Sanda, kuma babban baturen ƴan sanda da ke ƙaramar hukumar Tsanyawa a Kano mai suna SP Ibrahim Lado, inda suka kai su asibitin ƙwararru na ƙaramar hukumar Tsanyawa a Kano.

Continue Reading

Trending