Manyan Labarai
‘Yan sanda sun cafke gawurtaccen dan fashi

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta cafke wani gawurtaccen dan fashi da makami mai suna Ahmadu Rufa’i.
Baya ga fashi da makami, ana zargin Amadun da lafin sata da kuma yin garkuwa da mutane don neman biyan kudin fansa.
Kakakin rundunar ‘yan sanda ta jihar Katsina SP. Gambo Isa ne ya bayyana cewa bayan shafe tsawon lokaci suna neman sa, a karshe sun samu nasarar cafke Ahmadu Rufa’I dan asalin karamar hukumar Faskari ta jihar Katsina, dauke da bindiga, kuma nan bada jimawa ba zasu gurfanar da shi a gaban kotu.
Labarai
Ganduje ya bayar da umarnin rufe makarantun gaba da Sakandire Uku

Gwamnan Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayar da umarnin rufe wasu cikin makarantun gaba da Sakandiren jihar nan take.
Hakan na cikin wata sanarwa da Kwamishiniyar ilimi mai zurfi ta jiha Dr. Mariya Mahmud Bunkure ta fitar.
Makarantun da aka rufe sun haɗar da, Kwalejin share fagen shiga jami’a ta Rabi’u Musa Kwankwaso da ke Tudunwada.
Sai kuma Kwalejin nazarin tsaftar muhalli da ke garin Gwarzo, da kuma ta fasahar bunƙasa sana’o’in dogaro da ke garin Rano.
Rufewar ta kuma shafi Kwalejin nazarin harkokin noma da ke garin Ɗanbatta.
Ta cikin sanarwar Kwamishiniyar ta ce, an ɗauki wannan mataki ne sakamakon shawarwarin da aka bai wa Gwamnati, ɗalibai su gaggauta koma wa zuwa gida nan take.
Idan hali ya yi, Kwamishiniyar ta ce, za a sanar da ranar ci gaba da karatun.
Labarai
Rahoto: Mu kula da harshe domin guje wa illar sa – Limamin Kuntau

Limamin masallacin Juma’a na Ashabul Kahfi dake unguwar Kuntau Malam Munzali Bala Koki ya ce, al’umma su rinka kiyaye lafuzan su domin duk abinda mutum ya fada za a yi masa hisabi akan sa.
Malam Munzali ya bayyana hakan ne a hudubar Juma’a da ya gabatar a masallacin Ashabul Kahfi.
Ya na mai cewa, mu rinka kiyaye harshen mu domin kaucewa furta zai kai mu ga yin danasan, idan kuma bakin k aba zai fadi alheri ba to yayi shiru shi ne yafi.
Saurari wannan domin jin cikakken rahoton.
Labarai
Rahoto: Mawadata sai sun rinka tallafawa mabukata – Limamin Sani Mainagge

Limamin masallacin Juma’a na Jami’u Amiril Jaishi dake unguwar Sani Mainagge Mukhtar Abdulkadir Dandago ya yi kira ga madata da su rinka taimakawa wadanda ke da bukata ta hanyar ciyarwa da zakka domin samun dacewa da rahmar ubangiji.
Malam ya bayyana hakan ne yayin hudubar Juma’a da ya gabatar a masallacin Juma’a na Jami’u Amiril Jaishi.
Domin jin cikakken rahoton saurari wannan.
-
Manyan Labarai1 year ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Nishadi1 year ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai12 months ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Nishadi1 year ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai5 months ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi1 year ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai1 year ago
Ba’amurkiya da masoyin ta sun hada cinkoso a kasuwar Sabon Gari
-
Manyan Labarai1 year ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano