Connect with us

Manyan Labarai

Kano :Gobara ta tashi a gidaje daban-daban lokaci guda

Published

on

Wata gobara da ta kama a garin Tugugu dake karamar hukumar Bunkure a jihar Kano, ta yi sanadiyar kona gidaje guda hudu tare da tarin dukiya a ciki.

Gobarar dai wadda ta fara tashi da misalign karfe goma sha biyu na ranar Alhamis, ta kuma rinka yi wa gidajen dauki daidai da suke nesa da juna, har kusan karfe tara na daren ranar.

Wasu mazauna garin sun shaidawa Dala FM cewa ba a taba samun irin wannan annobar ta tashin gobara a yankin sai a wannan lokacin.

Yahaya Muhammad Rubben mazaunin garin ya ce” Har kawo yanzu ba mu san abun da ya haddasa gobarar ba, kuma ta lakume tarin dukiya mai yawa”. Yahaya.

Sagiru Ali ya na cikin wadanda suka taimaka a ka kasha gobarar ya ce” Mun sha wahala kafin mu kasha wutar, sakamakon muna nesa da cikin birni”.inji Aliyu.

Guda daga cikin magidancin da gobarar ta kama gidan sa, Muhammad Sani Danlami, ya ce” Gobarar ta kone ma na dakuna biyu, kuma tarin kayan mu ya na ciki tun daga kan kayan sawa da kayan abinci ba mu tsira da komai ba”. A cewar Muhammad.

Kan wannan batun ne muka tuntubi limamin masallacin Usman Bn Affan dake unguwar Kuntau a karamar hukumar Gwale a jihar Kano, Mallam Aminu Kidir Idris, ya ce”Wala Allah ko a na aikata sabo ne a yankin Allah ya jarrabe su”. Inji Kidir.

 

 

Baba Suda

Gwamnatin Kano ta musanta labarin da ke cewa za ta saka kafar Wando daya da Sojojin Baka

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ke yawo na cewa za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishinan yada labaran jihar Kwamred Ibrahim Waiya shi ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da hukumar kula da kafafen yada labarai NBC ta shirya a yau Alhamis.

 

Yace gwamnatin Kano za ta hada kai da Yan siyasa masu magana a Rediyo da aka fi Sani da Sojojin Baka, domin tsaftace harkokin siyasar Kano.

 

Haka kuma kwamishinan ya musanta labarin da ke cewa Gwamnatin Kano za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishina Waiya ya kuma ce za su hada kai da kafafen yada labarai domin Kara kawo tsafta a harkokin siyasar Kano.

Continue Reading

Manyan Labarai

Da Ɗumi-Ɗumi! Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers da mataimakin sa da ƴan majalisar jihar na watanni 6.

Published

on

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers Siminalayi Fubara, da mataimakiyar sa Mrs. Ngozi Odu, har na tsawon watanni 6.

Shugaba Tinubu ya bayyana daukar matakin ne a cikin wani taƙaitaccen jawabin sa da ya gabatar a cikin daren Talatar nan, ya ce ya yi amfani da damar da kundin tsarin mulki ya ba shi wajen sanya wannan doka wacce ta kwace mulkin jihar daga hannun gwamnan jihar Siminalayi Fubara da mataimakin sa har sai lamura sun dawo dai-dai a jihar.

Kazalika, shugaba Tinubu ya kuma bayyana dakatar da dukkanin ƴan majalisar dokokin jihar suma na tsawon watanni shidan, tare da sanya dokar ta ɓaci a jihar.

Wannan dai na zuwa ne biyo bayan rikicin siyasar da ya daɗe da kunno kai a tsakanin gwamna Fubara da ministan birnin tarayya Abuja Nyesome Wike, al’amarin da ya janyo takun saƙa tsakanin sa da ƴan majalisar dokokin jihar.

Continue Reading

Manyan Labarai

Isra’ila ta kashe sama da mutane 200 bayan karya yarjejeniyar tsagaita Wuta a Gaza

Published

on

Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, tare da ƙaddamar da sabbin hare-hare kan Falasdinawa.

Jaridar TRT Hausa ta ruwaito cewa, aƙalla Isra’ila ta kashe fiye da mutum 200 tare da jikkata ɗaruruwa a yayin da ake ci gaba da kai gawawwaki asibiti, kamar yadda majiyoyin wani asibiti a yankin Gaza suka bayyana.

Continue Reading

Trending