Manyan Labarai
Zabe: An jefa kuri’a a kan budurwa domin zabar miji

Wasu samari biyu sun jefa kuri’ar zabe kato bayan kato, bayan tsawon kwanaki uku ana yin kamfen, akan son wata bakar budurwa, ‘yar Bauchi dake garin Giyade, Hajara Muhammad.
Samarin, Yunusa Muhammad da Ibrahim Adamu, sun kamu ne da kaunar budurwar, wadda itama ta kamu da kaunar tasu, ta kuma umarce su da suje su kada kuri’ar zabe.
Bayan da aka sanar da Dattawan garin, sai aka kuma bude kofar kamfen tsawon kwanaki uku, wanda aka yi zaben karkashin kulawar jami’an tsaron garin, inda itama budurwar ta kai ziyarar gani da ido filin zaben.
Bayan kammala zaben, Yunusa Muhammad, shi ne ya yi nasara, an kuma ba shi tikiti, sakamakon lashe zaben da ya yi, sai dai amma shi wanda bai samu nasara ba, Ibrahim Adamu ya ce, “Bai yarda da zaben ba, tun da dai dama a kofar gidan abokin karawar ta wa a ka yi zaben, domin haka ya zama Inconclusive.” Inji Ibrahim.
Sai dai bamu samu zantawa da ango mai nasara Yunusa Muhammad ba, amma Aminsa Tajuddin Umar ya bayyana cewa, “Wanda ya fadin, ya rage nasa mu dai mun riga mun yi nasara, har ma mun fara shirye-shiryen fati.” A cewar aminin ango
Shima Sakataren zaben, Ibrahim Taldo Giyade, ya ce, “Tsakani da Allah mu kai zaben mu, domin dai har da jami’an tsaro ma a wajen, amma dai wanda ya fadin, mun ba shi wa’adin mako guda ya daukaka kara wurin mahukunta.”
Itama amaryar Hajara Muhammad, ta ce, “Koda dai nima ya sanar da ni bai gamsuba, amma dai a wurina zaben ya kammala, saura kuma sai abun da hukumar zaben ta aiwatar.”
Malam Aminu Kidir limamin masallacin Usman Bin Affan dake Kuntau karamar hukumar Gwale, ya yi bayanin matsayin irin wannan aure da samarin suka yi zasu zaben kuri’a a mahangar addinin musulinci da cewa, “Musulunci ya haramta nema cikin nema, domin haka ba ya halatta wani na neman aure wani kuma ya shigo, sai in wancan ya yi ikirarin ya janye, kuma wannan zaben da suka yi a kan budurwa babu aibu a kansa ko auren a ka yi ya yi, abun da a ke bukata kenan, yayin da samari suka hadu a kan budurwa to su yi kuri’a domin a fitar da mutum daya kwakkwara.” Inji Malam Kidir

Manyan Labarai
Ɗan Bijilante ya rasa ransa bisa arangamar su da wasu ƴan Daba a Kano

Ƙungiyar sintirin Bijilante ta ƙasa reshen jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin kwamandan ta Ubale Barau Muhammad Badawa, ta tabbatar da rasuwar guda daga cikin jami’in ta mai suna Suraj Rabi’u mazaunin Jaba da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar, sakamakon arangama da ƴan Daba.
Mai magana da yawun ƙungiyar Bijilante na jihar Kano, kuma Kwamandan ta na ƙaramar hukumar Fagge, Usman Muhammad Ɗan Daji, shi ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM Kano a ranar Lahadi.a
“Jami’in Bijilanten namu ya rasa ran nasa ne sakamakon arangama da suka yi da wasu Ƴan Daba yayin gudanar aikinsu a ranar Idin ƙaramar Sallah, inda ƴan dabar suka soke shi da Ɗanbida a Ƙirji da bayansa, wanda ya yi sanadiyar rasuwarsa, “in ji Usman”.
Ya kuma ce, an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi mai suna Usman Sharif mazaunin ƙaramar hukumar Dala, kuma tuni aka miƙa shi hannun jami’an tsaro.
Usman Ɗan daji, ya kuma yi addu’ar Allah ya jiƙan jami’in nasu ya gafarta masa.

Manyan Labarai
An ga watan ƙaramar Sallah a Najeriya – Sarkin Musulmi

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar na uku ya tabbatar da ganin jinjirin watan Shawwal a Najeriya, inda za a yi karamar Sallah gobe Lahadi.
Sarkin Musulmin ya bayyana hakan ne a yayin jawabin da ya gabatar a cikin daren Asabar ɗin nan, ya ce sun samu rahotannin ganin watan ne daga sassa daban-daban na ƙasar nan.
Alhaji Sa’ad Abubakar ya ce daga cikin guraren da aiko musu da ganin jinjirin watan na Shawwal akwai Zazzau, da kuma daga Sarkin Dutse, da Arugungu, da kuma Shehun Borno, da dai sauran gurare daban-daban na Najeriya.
Ya kuma yi kira ga al’ummar Musulmi da su gabatar da bikin sallar cikin kwanciyar hankali, tare da taimaka wa mabuƙata.
Tashar Dala FM Kano ta ruwaito cewa, biyo bayan sanarwar fadar mai alfarma Sarkin Musulmi, ya kasance ranar Lahadi take 1 ga watan Shawwal na shekarar 1446, wato ranar ƙaramar Sallah.

Manyan Labarai
Shugaba Tinubu da Sifeton Ƴan Sanda ku bi wa mutanen mu da aka yi wa kisan gilla hakƙin su – Rt. Hon. Rurum

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Rabo, Kibiya da Bunkure, Kabiru Alhassan Rurum, ya bayyana kaɗuwar sa bisa kisan gillan da aka yi wa wasu Mafarauta su kusan 16, a garin Uromi da ke jihar Edo, a lokacin da suke hanyar su ta komawa Kano daga jihar Rivers.
Honarable Kabiru Rurum, ya bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da aka aikowa Dala FM Kano a ranar Asabar, ya ce daga cikin mutanen da aka ƙona akwai mutum 11 da suka fito daga mazaɓun yankin sa na Kibiya da Bunkure, inda wasu 6 suka samu muggan raunuka suna karɓar Magani yanzu haka a jihar Edo.
A cewar Ɗan Majalisar, “Wannan abu da matasan garin Uromi a jihar Edo, suka yi ya saɓa da dokar kasa, kuma mummunan laifi ne, a don haka za mu bi kadin hakƙin mutanen mu da aka kashe a kuma waɗanda aka jikkata, “in ji shi“.
Kabiru Rurum, ya ce a matsayinsa na wakilin mutanen da aka kashe a majalisar Wakilai ta ƙasa, yana kira ga shugaban Najeriya Bola Tinubu, da babban Sifeton ƴan sanda, da su yi duk mai yiyuwa wajen ganin an kamo waɗanda suka yi wannan aika-aikar tare da hukunta su, da kuma biyan diyya ga iyalan waɗanda suka rasu da kula da waɗanda suka jikkata.
“Kasancewar wannan bashi ne na farko da ake samun wasu ɓata gari na tare matafiya akan hanya da basu ji ba basu gani ba su kashe su, a don haka muna fatan wannan karon gwamnati da sauran hukumomin tsaro za su ƙaddamar da ƙwaƙƙwaran bincike don ɗaukae mataki kamar yadda dokar kasa ta tanada, “in ji Rurum”.
Ɗan majalisar ya kuma jajantawa dukkanin al’ummar jihar Kano musamman Iyalan waɗanda suka rasu, tare da addu’ar Allah ya gafarta musu yasa Jannatul Firdausi makomar su, su kuma waɗanda suka jikkata Allah ya basu lafiya.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su