Manyan Labarai
Zabe: An jefa kuri’a a kan budurwa domin zabar miji
Wasu samari biyu sun jefa kuri’ar zabe kato bayan kato, bayan tsawon kwanaki uku ana yin kamfen, akan son wata bakar budurwa, ‘yar Bauchi dake garin Giyade, Hajara Muhammad.
Samarin, Yunusa Muhammad da Ibrahim Adamu, sun kamu ne da kaunar budurwar, wadda itama ta kamu da kaunar tasu, ta kuma umarce su da suje su kada kuri’ar zabe.
Bayan da aka sanar da Dattawan garin, sai aka kuma bude kofar kamfen tsawon kwanaki uku, wanda aka yi zaben karkashin kulawar jami’an tsaron garin, inda itama budurwar ta kai ziyarar gani da ido filin zaben.
Bayan kammala zaben, Yunusa Muhammad, shi ne ya yi nasara, an kuma ba shi tikiti, sakamakon lashe zaben da ya yi, sai dai amma shi wanda bai samu nasara ba, Ibrahim Adamu ya ce, “Bai yarda da zaben ba, tun da dai dama a kofar gidan abokin karawar ta wa a ka yi zaben, domin haka ya zama Inconclusive.” Inji Ibrahim.
Sai dai bamu samu zantawa da ango mai nasara Yunusa Muhammad ba, amma Aminsa Tajuddin Umar ya bayyana cewa, “Wanda ya fadin, ya rage nasa mu dai mun riga mun yi nasara, har ma mun fara shirye-shiryen fati.” A cewar aminin ango
Shima Sakataren zaben, Ibrahim Taldo Giyade, ya ce, “Tsakani da Allah mu kai zaben mu, domin dai har da jami’an tsaro ma a wajen, amma dai wanda ya fadin, mun ba shi wa’adin mako guda ya daukaka kara wurin mahukunta.”
Itama amaryar Hajara Muhammad, ta ce, “Koda dai nima ya sanar da ni bai gamsuba, amma dai a wurina zaben ya kammala, saura kuma sai abun da hukumar zaben ta aiwatar.”
Malam Aminu Kidir limamin masallacin Usman Bin Affan dake Kuntau karamar hukumar Gwale, ya yi bayanin matsayin irin wannan aure da samarin suka yi zasu zaben kuri’a a mahangar addinin musulinci da cewa, “Musulunci ya haramta nema cikin nema, domin haka ba ya halatta wani na neman aure wani kuma ya shigo, sai in wancan ya yi ikirarin ya janye, kuma wannan zaben da suka yi a kan budurwa babu aibu a kansa ko auren a ka yi ya yi, abun da a ke bukata kenan, yayin da samari suka hadu a kan budurwa to su yi kuri’a domin a fitar da mutum daya kwakkwara.” Inji Malam Kidir
Manyan Labarai
Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu ya naɗa Hakimai Shida
Mai martaba sarkin Kano Dakta Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu, ya naɗa hakimai shida da safiyar Juma’ar nan tun bayan dawo da shi a matsayin Sarki.
Sarkin ya naɗa Alhaji Abba Yusuf baffan gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf a matsayin Ɗan Makwayon Kano, da Alhaji Auwalu Mudi Yakasai, shi kuma Ɗan Malikin Kano, da Abdulƙadir Muhammad Balarabe a matsayin Zannan Kano.
Sauran sune Alhaji Muhktar Ibrahim Bello da Sarkin ya naɗa shi a matsayin Falakin Kano, sai kuma Alhaji Aminu Abdullahi Nasidi a matsayin Galadiman Kano.
Wakilin Dala FM Kano Yakubu Ibrahim Doragarai ya ruwaito ya ruwaito cewa, tuni hakiman da aka naɗa suka yi gaisuwa ga Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu.
Manyan Labarai
Jam’iyyar NNPP ta dakatar da sakataren gwamnatin Kano da wani Kwamishina
Jam’iyyar NNPP ta jihar Kano ta bayyana dakatar da sakataren gwamnatin jihar Dakta Abdullahi Baffa Bichi, da Kwamishinan Sufuri na jihar Kano Muhammad Diggwal, daga cikin jam’iyyar.
Shugaban jam’iyyar NNPP a Kano Dakta Hashim Sulaiman Dungurawa ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da aka aikowa Dala FM Kano, a cikin daren yau Litinin.
Hashim Dungurawa, ya ce dakatar da ƙusoshin gwamnatin jihar Kano su biyu ya biyo bayan zargin keta alfarmar jagoranci, da ta Jam’iyya, da kuma keta alfarmar gwamnati, a don haka ne suka ɗauki matakin ba tare da yin wasa ba akai.
“Jagorancin shugabancin jam’iyyar mu na ƙananan hukumomin da mutane biyun suka fito sun gabatar mana da ƙorafe-ƙorafe kan ƙusoshin gwamnatin biyu, akan zarge-zarge da ake musu ya sa muka ɗauki matakin dakatar da su, har sai mun gama bincike, “in ji Dungurawa”.
Sulaiman ya ƙara da cewar dakatar da Abdullahi Baffa Bichi da Muhammad Diggwal ta fara aiki ne daga ranar Litinin 14 ga watan Oktoban 2024, kamar yadda jam’iyyar ta samu ingantattun shawarwari akan zargin da ake musu.
Manyan Labarai
Ku tallafawa mazauna Asibitin masu lalurar Ƙwaƙwalwa na Ɗorayi bisa halin da suke ciki – Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam
Ƙungiyar wayar da kan jama’a da kare haƙƙin ɗan adam da tallafawa mabuƙata, ta Awareness for Human Right and Charity Foundation, ta tallafawa mazauna Asibitin masu lalurar Ƙwaƙwalwa da ke unguwar Ɗorayi, da dafaffen abinci, domin rage musu wata damuwa.
Ƙungiyar dai ta rabawa masu lalurar Ƙwaƙwalwar abincin ne da yammacin Asabar 12 ga watan Oktoban 2024, tare da ziyartar wata makarantar tsangaya da ke unguwar Ɗorayi, inda ɗalibai 1,000 suka rabauta da tallafin dafaffen abincin.
Da yake yiwa Dala FM Kano, ƙarin bayani daraktan ƙungiyar ta Awareness for Human Right and Charity Foundation, Kwamared Auwal Usman, ya ce rahotannin da suka samu kan yadda mazauna Asibitin da kuma makarantun tsangayar ke fuskantar ƙalubalen abinci ya sa suka kai musu tallafin domin rage musu wani raɗaɗi.
Wasu daga cikin masu lalurar Ƙwaƙwalwar da suka fara samun sauƙi, sun nemi ɗaukin gwamnatin jihar Kano wajen magance ƙalubalen da suke fuskanta na rashin kyawun wuraren da suke kwana da sauran matsaloli, ko sa samu wani sauƙi.
Da yake nasa jawabin mai kula da Asibitin da ake kula da masu lalurar Ƙwaƙwalwar na Ɗorayi a Kano, Munnir Ɗahiru Kurawa, ya miƙa godiyar sa ga tawagar ƙungiyar bisa kaɓakin alkhairin da ta saukewa masu taɓin hankalin.
Wannan dai na zuwa ne makwanni kaɗan da gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya ziyarci Asibitin masu lalurar Ƙwaƙwalwar na Ɗorayi, har ma ya bada umarnin aje a gyara shi, sai dai kawo yanzu hakan bata samu ba kamar yadda wata majiya ta bayyana.
-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya2 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su