Connect with us

Manyan Labarai

Zabe: An jefa kuri’a a kan budurwa domin zabar miji

Published

on

Wasu samari biyu sun jefa kuri’ar zabe kato bayan kato, bayan tsawon kwanaki uku ana yin kamfen, akan son wata bakar budurwa, ‘yar Bauchi dake garin Giyade, Hajara Muhammad.

Samarin, Yunusa Muhammad da Ibrahim Adamu, sun kamu ne da kaunar budurwar, wadda itama ta kamu da kaunar tasu, ta kuma umarce su da suje su kada kuri’ar zabe.

Bayan da aka sanar da Dattawan garin, sai aka kuma bude kofar kamfen tsawon kwanaki uku, wanda aka yi zaben karkashin kulawar jami’an tsaron garin, inda itama budurwar ta kai ziyarar gani da ido filin zaben.

Bayan kammala zaben, Yunusa Muhammad, shi ne ya yi nasara, an kuma ba shi tikiti, sakamakon lashe zaben da ya yi, sai dai amma shi wanda bai samu nasara ba, Ibrahim Adamu ya ce, “Bai yarda da zaben ba, tun da dai dama a kofar gidan abokin karawar ta wa a ka yi zaben, domin haka ya zama Inconclusive.”  Inji Ibrahim.

Sai dai bamu samu zantawa da ango mai nasara Yunusa Muhammad ba, amma Aminsa Tajuddin Umar ya bayyana cewa, “Wanda ya fadin, ya rage nasa mu dai mun riga mun yi nasara, har ma mun fara shirye-shiryen fati.”  A cewar aminin ango

Shima Sakataren zaben, Ibrahim Taldo Giyade, ya ce, “Tsakani da Allah mu kai zaben mu, domin dai har da jami’an tsaro ma a wajen, amma dai wanda ya fadin, mun ba shi wa’adin mako guda ya daukaka kara wurin mahukunta.”

Itama amaryar Hajara Muhammad, ta ce, “Koda dai nima ya sanar da ni bai gamsuba, amma dai a wurina zaben ya kammala, saura kuma sai abun da hukumar zaben ta aiwatar.”

Malam Aminu Kidir limamin masallacin Usman Bin Affan dake Kuntau karamar hukumar Gwale, ya yi bayanin matsayin irin wannan aure da  samarin suka yi zasu zaben kuri’a a mahangar addinin musulinci da cewa, “Musulunci ya haramta nema cikin nema, domin haka ba ya halatta wani na neman aure wani kuma ya shigo, sai in wancan ya yi ikirarin ya janye, kuma wannan zaben da suka yi a kan budurwa babu aibu a kansa ko auren a ka yi ya yi, abun da a ke bukata kenan, yayin da samari suka hadu a kan budurwa to su yi kuri’a domin a fitar da mutum daya kwakkwara.” Inji Malam Kidir

Manyan Labarai

Bamu da wata alaƙa akan dakatar da Ganduje daga jam’iyyar APC – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya ce basu da wata alaƙa da rikicin cikin gidan da ya kunno kai akan dakatar da Ganduje daga cikin jam’iyyar APC, a Kano.

Babban daraktan yaɗa labaran gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM a yau Laraba.

Ya ce zargin da jam’iyyar APCn Kano ta yi a kan gwamnatin Kano, kan cewar tana da hannu akan dakatar da shugaban ta na riƙo a matakin ƙasa Abdullahi Umar Ganduje, zargin bashi da tushe ballantana makama.

A baya-bayan nan ne dai wani sashi na shugabancin jam’iyyar APC, a mazaɓar Ganduje da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa, ya bayyana dakatar da Abdullahi Ganduje daga cikin jam’iyyar.

Sai dai daga bisani shugaban jam’iyyar na ƙaramar hukumar ya musanta batun dakatarwar inda ya ce ana shirin ɗaukar matakin da ya dace akan wanda ya fitar da sanarwar.

Bature, ya kuma ce lamarin rikici ne na cikin gidan jam’iyyar ta APC, wanda ya kamata su tsaya su gyara, mai-makon mayar da hankali akan gwamnatin Kano, lamarin da ba za suyi nasara ba.

“Tsagin jam’iyyar APCn, Kano suje can kada su ƙara tsomo mu a cikin rikicin su domin bamu da alaƙa da wani rikicin su ko wani abu, “in ji Sunusi”.

Ya kuma ce ko da yaushe jam’iyyar NNPP, mai mulki a jihar Kano burin su shine ci gaba da taimakawa al’ummar jihar ta hanyar damar da ayyukan ci gaban su.

Dawakin Tofa, ya kuma ƙara da cewa Ganduje bashi da tasiri ko da a ƙaramar hukumar sa ballantana kuma azo batun jahar Kano.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Manyan Labarai

Jam’iyyar NNPP ta dakatar da Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf

Published

on

Tsagin jam’iyyar NNPP ta ƙasa karkashin jagorancin Major Agbo, ya sanar da dakatar da Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf daga cikin jam’iyyar.

A cikin wata sanarwa da sakataren jam’iyyar ta ƙasa Ogini Olaposi, ya fitar a yayin taron ‘yan jarida a Talatar nan a Abuja, tsagin jam’iyyar ta NNPP, ya ce rashin bayyana a gaban kwamitin ladabtarwar jam’iyyar da Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi shine ya sanya su ɗaukar wannan mataki.

Ya ƙara da cewa matakin na zuwa ne sakamakon fusata da jam’iyyar ta yi kan halartar wani babban taron jam’iyyar da gwamnan ya yi wanda tsagin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya jagoranta a ranar 6 ga watan Afrilun nan na shekarar 2024. kamar yadda jaridar THE PUNCH ta rawaito.

Sai dai tuni wasu ƴan Kwankwasiyyar suka yi watsi da wannan dakatarwa.

Dambarwar dai na zuwa ne yayin da itama jam’iyyar APC, ke ci gaba da fuskantar ta ta dambarwar, musamman ma da aka jiyo yadda wani sashi na shugabancin jam’iyyar a mazaɓar Ganduje a ƙaramar hukumar Dawakin Tofa, aka jiyo shi ya dakatar da shugaban riƙo na APC ta ƙasa Abdullahi Umar Ganduje, daga cikin jam’iyyar.

Sai dai daga bisani shugabancin jam’iyyar ta APC, a ƙaramar hukumar Dawakin Tofa, ya musanta batun dakatarwar lamarin da yace ma ana shirye-shiryen ɗaukar mataki akan waɗanda suka bayyana dakatarwar.

Continue Reading

Trending