Connect with us

Labarai

Za a fara daukar mataki a kan masu yada tsiraici

Published

on

Limamin masallacin juma’a na Usman Bin Affan dake Unguwar Kuntau Mallam Aminu Kidir Idris, ya yi kira ga al’ummar musulmai da su guji yada barna a doron kasa domin gudun fishin Allah (S.W.T)’

Mallam Aminu kidir, ya yi wannan kiran ne jim kadan bayan fitowa daga cikin shirin Shari’a a aikace na nan Gidan Rediyon Dala da safiyar yau Alhamis.

Yana mai cewa,”fitar da barna ga al’umma a gari ka iya janyo fishin Ubangiji S.W.T, domin haka akwai bukatar jama’a su kiyaye yin hakan, zai fi kyautatuwa mutane su rinka addua mai makon yadawa”.

Da yake nasa tsokacin a kan wani fai-fan bidiyo da a ka wallafa na yar wasan hausar nan Maryam Booth, a kafafen sada zumunta, shugaban gamayyar kungiyoyin kare hakkin dan Adam ta Humman Right Network Kwamred A-A Haruna Agayi, ya ce”Tun bayan da fai-fan bidiyon ya bulla mu ke kokari wajen ganin an nemawa mai hakki hakkin sa”. Inji AA Ayagi.

Wakilin mu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa, Kwamred A-A Haruna Ayagi, ya kuma ja hankalin wadanda suke yada bidiyo dama hotunan mutane da su dai na, domin kuwa duk wanda ya shiga hannun su sukan dauki matakin kai shi wajen jami’an tsaro domin daukan matakin da ya dace a kansa.

Labarai

Mun dawo da Alhazan da suka gamu da rashin lafiya yayin aikin hajjin bana – NAHCON

Published

on

Hukumar kula da aikin Hajji ta kasa NAHCON, ta dawo da wasu Alhazan ta na jihohi uku waɗanda suka gamu da rashin lafiya a kasar Saudi Arebia, yau Litinin, sakamakon samun lafiyar da suka yi.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar NAHCON ta ƙasa, Musa Ubandawaki ya fitar a yau Litinin, jim kadan bayan Alhazan sun sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke birnin tarayya Abuja, a ƙarƙashin jagorancin shugaban hukumar Malam Jalal Ahmad Arabi.

Ta cikin sanarwar Ubandawaki, ya ce Alhazan jihohin uku da suka gamu da rashin lafiya a kasa mai tsarki, sun haɗar da Muhammad Sulaiman daga jihar Katsina, da Abubakar Sadik daga Kaduna, sai kuma Hajiya Aisha daga jihar Sokoto.

Sanarwar ta ce Alhazan sun gamu da rashin lafiya ne a kasar bayan sun kammala ibadar aikin Hajjin daya gabata na 2024, wanda aka kwantar dasu a Asibiti inda suka samu kulawar likitoci, kuma izuwa yanzu sun warke wanda hakan yasa NAHCON ta dawo dasu gida Najeriya.

Wakilinmu Abdulkarim Muhammad Abdulkarim ya ruwaito cewa, a aikin hajjin bana an samu yawaitar masu fama da matsalar rashin lafiya, sai dai an alaƙanta rashin lafiyar ne da yadda aka samu zafin rana a ƙasar Saudiyar.

Continue Reading

Labarai

Mun kulle Asibitoci masu zaman kan su 12 a Kano – PHIMA

Published

on

Hukumar da ke kula da Asibitoci masu zaman kan su ta jihar Kano PHIMA, ta ce zata ci gaba da daukar mataki akan dukkanin Asibitocin da suka saɓa ƙa’idar aiki, domin tsaftace harkar tare da samun damar kulawa da marasa lafiya cikin ka’ida.

Shugaban hukumar ta PHIMA, a nan Kano Farfesa Salisu Ahmad Ibrahim, ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, a ranar Juma’a 05 ga watan Yunin 2024.

Farfesa Salisu Ahmad, ya kuma ce daga zuwan sa hukumar zuwa yanzu aƙalla sun kulle Asibitoci guda 12, kuma akwai uku daga ciki an cire su daga tsarin asibitoci gaba ɗaya bisa sablɓa ka’idar aiki.

“Zamu ɗauki mataki akan dukkanin masu magungunan gargajiyar da suke zagayawa cikin unguwanni suna damun mutane da karar amsa kuwa, ko kuma bayyana batsa ta hanyar tallata magungunan nasu, domin tsaftace harkar, in ji Salisu”.

Wakilinmu Abdulkadir Muhammad Sani Tukuntawa ya rawaito cewa Farfesa Salisu Ahmad Ibrahim, ya kara da cewa yanzu haka hukumar ta PHIMA, tayi nisa wajen yiwa masu magungunan gargajiya
rijista tare da tantance su, domin tsarkake harkar da kuma gujewa fuskantar matsala.

Continue Reading

Labarai

Jami’an mu ku gujewa karɓar cin hanci da rashawa yayin aiki – Immigration

Published

on

Shugabar hukumar da ke kula da shige da fice ta kasa Immigration, Kemi Nanna Nandap, ta bukaci jami’ansu da su kaucewa karbar cin hanci da Rashawa a iyakokin kasa, tare da aiki tuƙuru yayin da suke gudanar da ayyukansu a iyakokin Najeriya.

Shugabar Kemi Nanna, da ta samu wakilcin HK Usman, yayin taron da hukumar kula da shige da ficen reshen jihar Kano Immigration, ta gudanar yau a hedikwatar ta, inda ta kaddamar da yaki da cin hanci da rashawa a tsakanin jami’an hukumar da kuma al’umma.

Ta kuma ce kaddamar da al’amarin zai taimaka wajen daƙile cin hanci da
rashawa a tsakanin jami’an su da kuma al’umma musamman ma a iyakokin kasar nan da kuma ofisoshin da suke aiki.

“Nasan mu masu tsaron ƙasa ne musamman ma a iyakokin ƙasa, dole ne mu yi abinda ya kamata wajen daƙile cin hanci da rashawa a cikin aikin mu: kuma jami’an mu idan suka yi aiki tuƙuru za’a samu nasara, “in ji shi”.

Da yake nasa jawabin shugaban hukumar kula da shige da fice Immigration, ta kasa reshen jihar Kano, Ibrahim Muhammad Abubakar, ya ce sun shirya taron ne domin ƙaddamar da kawar da cin hanci da rashawa a cikin aikin nasu, kasancewar ba abu ne mai kyau ba.

Ya kuma nemi goyon bayan al’ummar ƙasar nan wajen magance harkokin cin hanci da rashawa, musamman ma tsakanin su da jami’an hukumar.

Wakilin Dala FM Kano, Hassan Mamuda Ya’u ya ruwaito cewa taron ya samu halartar jami’an hukumar da dama ciki har na birnin tarayya Abuja, da kuma jami’an tsaro, kuma ciki har da jami’an hukumar kula da gidan gyaran hali na jihar Kano, da na rundunar tsaro ta Civil Defense, da kuma hukumomin gwamnati da dai sauran su.

Continue Reading

Trending