Labarai
Za a fara daukar mataki a kan masu yada tsiraici

Limamin masallacin juma’a na Usman Bin Affan dake Unguwar Kuntau Mallam Aminu Kidir Idris, ya yi kira ga al’ummar musulmai da su guji yada barna a doron kasa domin gudun fishin Allah (S.W.T)’
Mallam Aminu kidir, ya yi wannan kiran ne jim kadan bayan fitowa daga cikin shirin Shari’a a aikace na nan Gidan Rediyon Dala da safiyar yau Alhamis.
Yana mai cewa,”fitar da barna ga al’umma a gari ka iya janyo fishin Ubangiji S.W.T, domin haka akwai bukatar jama’a su kiyaye yin hakan, zai fi kyautatuwa mutane su rinka addua mai makon yadawa”.
Da yake nasa tsokacin a kan wani fai-fan bidiyo da a ka wallafa na yar wasan hausar nan Maryam Booth, a kafafen sada zumunta, shugaban gamayyar kungiyoyin kare hakkin dan Adam ta Humman Right Network Kwamred A-A Haruna Agayi, ya ce”Tun bayan da fai-fan bidiyon ya bulla mu ke kokari wajen ganin an nemawa mai hakki hakkin sa”. Inji AA Ayagi.
Wakilin mu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa, Kwamred A-A Haruna Ayagi, ya kuma ja hankalin wadanda suke yada bidiyo dama hotunan mutane da su dai na, domin kuwa duk wanda ya shiga hannun su sukan dauki matakin kai shi wajen jami’an tsaro domin daukan matakin da ya dace a kansa.

Labarai
Mu taimaka wa masu ƙaramin ƙarfi domin rage musu raɗaɗin rayuwa – Ambada Muhammad

Shugaban ƙungiyar mu haɗa zumunci ta KHZ Foundation dake nan Kano Ambasada Dakta Muhammad Abdulsalam, ya ce, taimakawa masu ƙaramin ƙarfi musamman a wannan lokaci na watan Azumin Ramadana, zai taimaka musu wajen rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.
Ambasada Muhammad Abdulsalam ya bayyana hakan ne a yayin taron baiwa iyayen marayu da masu ƙaramin ƙarfi tallafin kayan abinci a ofishin kungiyar yau Litinin, da kuma basu a wasu unguwanni da suka haɗar da Tukuntawa da Sabuwar Gandu, Tinshama da dai sauransu.
Ya kuma ce, kamata yayi al’umma su ƙara himma wajen shiga makamancin ƙungiyar su domin baiwa al’umma gudunmawar da ta kamata, ta hanyoyi daban-daban, domin cire musu wata damuwa da ta damesu a rayuwa.
“Zamu fitar da ɗaurarru masu ƙananan tara a wasu gidjen ajiya da gyaran hali domin fitar da su daga halin rayuwar da suke ciki na jarrabta da suka tsinci kan su”. In ji Ambasada Muhammad.
Da yake nasa jawabin malami a kwalejin ilmin tarayya ta FCE dake nan Kano Mallam Ibrahim Muhammad Gandu, gargaɗar iyayen marayun da sukaci gajiyar tallafin yayi, da su yi amfani da kayayyakin abincin ta hanyar da ta dace Mai-makon siyar da kayan a ƙasƙance da ake zargin wasu suna yi a wasu lokutan.
Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewar, iyayen marayu da masu ƙaramin ƙarfi da dama ne suka rinƙa bayyana farin cikinsu, bisa basu kayan abincin da akayi, wanda suka haɗar da Shinkafa, Gero Taliya Man girki da sai sauransu, haɗi da Naira dubu ɗaya kuɗin Mota ga kowannen su.

Labarai
Ɗaurarru sama da dubu 1 aka duba lafiyar su a Kano

Ɗaurarru sama da dubu ɗaya ne dake zaune a gidajen gyaran hali na goron Dutse da Kurmawa a jihar Kano, suka amfana da ganin likitoci daban-daban tare da ba su magani kyauta.
Yayin wani aikin sa kai da nufin neman lada a wajan Allah da tawagar ƙungiyar likitoci musulmi suka yi, ƙarƙashin jagarancin shugaban kwanitin gudanar da aikin Dr. Sule Abdullahi Gaya.
Har ma shugaban ƙungiyar na jihar Kano, Dr. Muhammad Auwal ya ce, suna yin aikin ne domin taimakawa marasa ƙarfi a wurare daban-daban, tare da basu kayan abinci da ruwa, da makamantan su.
A jawaban su daban-daban Dr. Anas Ibrahim Yahaya Bichi da Dr. Muhammad Lawan Adamu waɗanda suna cikin likitocin da suka duba marasa lafiya da dama cewa suka yi, a tafiyar ta su babu irin likitan da babu, don haka kowacce irin cuta suka ci karo da ita sun tanadi maganin ta.
Daga bisani mai kula da gidan gyaran halin na Kurmawa DC Mu’azu Tukur wanda ya yi jawabi a madadin shugaban hukumar ya nuna godiya da jin dadin su kan aikin da kungiyar likitoci musulmi suka yi ga daurarrun.

Labarai
Tallafawa masu ƙaramin ƙarfi na rage musu raɗaɗin rayuwa – Kwamared Galadanchi

Shugaban ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Universal Declaration of Human Right Network dake nan Kano Kwamared Umar Sani Galadanchi, ya ce tallafawa masu ƙaramin ƙarfi gida hanya da na Asibiti yakan tallafa musu wajen rage musu wani raɗaɗin rayuwa da yake damunsu.
Kwamared Umar Galadanchi ya bayyana hakan ne a yayin da tawagar su ta sauke kayan shan ruwa ga marasa lafiya a wasu ɓangare na Asibitin Murtala dake nan Kano a ranar Lahadi.
Yana mai cewa, sun kaiwa marasa lafiyar kayan shan ruwan ne domin rage musu wata damuwa da take damunsu na yau da kullum.
“Yana daga cikin wajibcin aikace-aikacen ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam su tallafawa masu ƙaramin ƙarfi da lafiya, karfi da kuma aljihu domin ragewa mutane wata damuwa da take damun su”. Inji Umar Galadanchi.
Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa Umar Sani Galadanchi, ya kuma yi kira ga masu zuciya da su ƙara taimakawa al’umma musamman ma a wannan lokaci na Azumin watan Ramadan da ake ciki, da ake matuƙar buƙatar Mai-makon kashe dukiyoyin ta hanyar da basu da ce ba.

-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Manyan Labarai3 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai3 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi4 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai3 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya1 year ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Nishadi4 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai3 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano