Labarai
Za a fara daukar mataki a kan masu yada tsiraici

Limamin masallacin juma’a na Usman Bin Affan dake Unguwar Kuntau Mallam Aminu Kidir Idris, ya yi kira ga al’ummar musulmai da su guji yada barna a doron kasa domin gudun fishin Allah (S.W.T)’
Mallam Aminu kidir, ya yi wannan kiran ne jim kadan bayan fitowa daga cikin shirin Shari’a a aikace na nan Gidan Rediyon Dala da safiyar yau Alhamis.
Yana mai cewa,”fitar da barna ga al’umma a gari ka iya janyo fishin Ubangiji S.W.T, domin haka akwai bukatar jama’a su kiyaye yin hakan, zai fi kyautatuwa mutane su rinka addua mai makon yadawa”.
Da yake nasa tsokacin a kan wani fai-fan bidiyo da a ka wallafa na yar wasan hausar nan Maryam Booth, a kafafen sada zumunta, shugaban gamayyar kungiyoyin kare hakkin dan Adam ta Humman Right Network Kwamred A-A Haruna Agayi, ya ce”Tun bayan da fai-fan bidiyon ya bulla mu ke kokari wajen ganin an nemawa mai hakki hakkin sa”. Inji AA Ayagi.
Wakilin mu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa, Kwamred A-A Haruna Ayagi, ya kuma ja hankalin wadanda suke yada bidiyo dama hotunan mutane da su dai na, domin kuwa duk wanda ya shiga hannun su sukan dauki matakin kai shi wajen jami’an tsaro domin daukan matakin da ya dace a kansa.

Baba Suda
Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.
Cikakken labarin na Zuwa….

Baba Suda
Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.
Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.
Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

Baba Suda
NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.
Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.
A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.
Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

-
Nishadi6 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su