Connect with us

Labarai

An yi ram da likitar bogi a Kano

Published

on

A cigaba da zagayen tantance nagartar ayyukan lafiya a birnin Kano da kewaye, hukumar dake sanya ido kan asibitoci masu zaman kansu (PHIMA) ta bankado asirin wata likitar bogi a ranar Alhamis 20-02-2020.

Da yake jawabi ga manema labarai, babban sakataren hukumar, Dakta Usman Tijjani Aliyu, ya bayyana cewa sun gudanar da zagayen ne da hadin gwiwar bangaren mata na asibitin Abdullahi Wase, inda suka samu nasarar bankado asirin wata likitan bogi mai suna Samira Abubakar.

Dakta Usman ya ce” Likitar bogin na amfani da lasisin ma’aikaciyar jinya ta na gudanar da aikin fida da zubar da ciki ga masu juna biyu. Baya ga cajin marasa lafiya kudade da suka wuce kima. Likitar ta bogin na amfani da dalibai masu matakin karatu na sakandire a matsayin ma’aikatan jinya a asibitin na ta mai suna ‘Family Maternity’ dake yankin ‘Yan Kaba a kan titin Hadeja. Yanzu mun kulle asibitin domin baiwa ‘yan sanda damar gudanar da bincike a gabanin gurfanar da wanda a ke zargin a gaban kotu, duk da cewa ta cika wandon ta da iska lokacin da tawagar hadin gwiwar suka yiwa asibitin dirar mikiya”. Dakta Usman.

 

Baba Suda

‘Yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki – Minista

Published

on

Ministan Wutar Lantarki, Adedayo Adelabu ya bayyana cewa kimanin ’yan Najeriya miliyan 150 ne yanzu ke samun isasshiyar wutar lantarki, yayin da miliyan 80 ke da ƙarancin wutar lantarki.

 

Ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a yayin taron sabunta sassan ministoci na 2025 da aka gudanar a Abuja, inda ya yi magana tare da ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris Malagi, da sauran masu ruwa da tsaki.

 

Adelabu ya bayyana cewa ci gaban ya samo asali ne daga shigar Najeriya cikin shirin “Mission 300” – wani gagarumin ƙoƙarin haɗin gwiwa na Bankin Duniya da Bankin Raya Afirka (AfDB) da nufin samar da wutar lantarki ga ‘yan Afirka miliyan 300 nan da shekarar 2030.

 

Ƙa’idar ta tsara kyawawan manufofi don haɓaka hanyoyin samar da wutar lantarki, ƙara haɓaka makamashi da inganta hanyoyin magance matsalolin dafa abinci mai tsafta ga miliyoyin ‘yan Najeriya – wato Mission 300, kuma muna samun ci gaba mai kyau a kan wannan,” in ji shi.

 

Ya ci gaba da cewa, “Ina mai farin cikin gaya muku cewa cikin ‘yan Afirka miliyan 300 da Bankin Duniya da AfDB ke son cimmawa, Najeriya na kan hanyar da za ta biya ƙasa da kashi 25 cikin 100, wanda ke nufin kusan ‘yan Najeriya miliyan 75. Da muka gabatar da yarjejeniyarmu, sun amince da mu.”

Continue Reading

Daurin Boye

Mun kafa kwamiti domin rage farashin – Gwamnatin tarayya

Published

on

Gwamnatin tarayya ta kafa wani kwamiti da zaiyi Duba kan hanyoyin shigo da abinci domin rage farashin sa da kaso 50.

Kwamitin dai dake karkashin mataimakin shugaban kasa Sanata Kashim Shettima zai yi aiki ne da wasu ministoci, domin ganin an wadatar Nigeria da abinci.

 

Yayin jawabin sa, Sanata Kashim Shettima yace hakan wani bangare NE na kara inganta tattalin arziki da shugaban kasa Asuwaju Bola Tinubu ke kokari.

 

Continue Reading

Labarai

Arsenal ba kanwar lasa ba ce – Me tsaron Gidan Real Madrid

Published

on

Me tsaron Gidan kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid Thibaut Courtois yace sun yi rashin nasara ne a wasan da suka buga a jiya da kungiyar kwallon kafa ta Arsenal, saboda Arsenal din ba kanwar lasa ba ce.

A jiya Laraba ne dai aka fafata wasan kusa da na kusa da na karshe, tsakanin kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid da kuma Arsenal Inda Arsenal ta lallasa Real Madrid da ci 2 da 1.

Continue Reading

Trending