Connect with us

Labarai

An bada belin Mustapha Jarfa  

Published

on

A Alhamis din nan ne 20-02- 2020, kotun majistrate mai lamba 47 dake zaman ta a unguwar Gyadi-Gyadi ta sanya dan siyasan nan Mustapha Jarfa a hannun beli, bisa sharadin cewa sai ya kawo mai mataki na 14 a aikin gwamnati ko a karamar hukumar ko jiha ko kuma a tarayya tare da mutumin da ya biya haraji na shekara biyar, sharadi na uku shi ne ba zai yi magana a wata kafar sadarwa ba har sai an gama shari’ar. Idan kuma ya tserewa kotu wadanda suka tsaya masa za su biya naira dubu dari bibiyu.

Sai dai kasancewar bai cika sharudan ba, an sake mai da shi gidan ajiya da gyaran hali, inda a ka damka shi a hannun jami’in gidan, Babangida Sani da masu taimaka masa Nasir Ado da Mubarak Sani Karkarna.

Tun da fari dai a na zargin sa ne da tayar da hargitsi a cikin al’umma da barazana ga rayuwar mataimakin gwamnan Kano, Nasir Yusuf Gawuna da kuma bata masa suna harda zagi da cin mutuncin mataimakin gwamnan, ya kuma amsa laifin inda waccan lokutan majistrate mai lamba 34 ta yi masa hukuncin daurin shekara guda a gidan ajiya da gyaran hali ba kuma tare da zabin biyan tara ba.

A baya dai an gurfanar da shi ne a gaban kotun majistrate, mai lamba 34, dake zaman ta a Rijiyar zaki, inda yanzu kuma a ka canja masa kotun. Kamar yadda wakilin mu Abubakar sabo ya rawaito.

 

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending